Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025
Published: January 29, 2026 at 8:05 AM | By: Bala Hassan

Hukumar ladabtarwa ta CAF ta kakabawa hukumar kwallon kafa ta Senegal FSF, da hukumar kwallon ta Moroko takunkumi.

Hukumar ladabtarwa ta (“CAF”) ta sanya takunkumi kan Senegal da Moroko da wasu ‘yan wasa da jami’ai game da abubuwan da suka faru a lokacin gasar cin kofin Afirka na CAF na Moroko 2025, wanda ya keta ka’idojin CAF.

Hukumar ladabtarwa ta CAF ta dauki matakai kamar haka:

Game da Hukumar Kwallon Kafa ta Ƙasar Senegal (FSF), Hukumar Ladabtarwa ta CAF ta yanke shawarar dakatar da Mr Pape Bouna Thiaw, Babban Kocin Kungiyar Kwallon Kafa ta Senegal, na wasanni biyar (5) Wacce CAF ta shirya saboda rashin da’a da a wasan karshe wanda ya saba wa ka’idojin dokar CAF da kuma kawo rashin mutunta wasan an kuma ci Pape Bouna Thiaw tarar dalar Amurka 100,000.

Bayan haka CAF ta dakatar da dan wasan Senegal, Iliman Cheikh Baroy Ndiaye na wasanni biyu (2) na CAF, saboda rashin da’arsa ga alkalin wasa, CAF ta dakatar da dan Senegal, Ismaila Sarr na wasanni biyu (2) na CAF shima saboda rashin da’a da ya yi wa alkalin wasa.

Ita ma hukumar kwallon kafa ta Ƙasar Senegal (FSF), an ci tararta dala 300,000 saboda rashin da’a da magoya bayanta, suka nuna a ranar wasan wanda ya karya ka’idojin CAF na yin wasa mai kyau da mutunci, da kuma karin tarar dala 300,000 saboda rashin da’a daga ‘yan wasansu da ma’aikatan horaswa wanda CAF ta bayyana shi a matsayin rashin mutunta wasan.

Akwai tarar ga (FSF), dala 15,000 saboda rashin da’a na kungiyarta ta Ƙasar, saboda biyar (5) cikin ‘yan wasanta sun sami gargadi.

A bangaren Hukumar Kwallon Kafa ta Ƙasar Moroko (FRMF), Hukumar Ladabtarwa ta CAF ta yanke shawarar

dakatar da dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Moroko, Achraf Hakimi na wasanni biyu (2) na hukumar CAF, tare da dakatar da wasa daya (1) na tsawon shekara daya (1) daga ranar da aka yanke wannan hukunci, saboda rashin da’a da ya yi a wasan, bayan haka CAF ta dakatar da dan wasan kungiyar kwallon kafa na Moroko Ismaël Saibari wasanni uku (3) na hukumar CAF shima saboda rashin da’arsa an kuma ci Ismaël Saibari tarar dala 100,000.

CAF ta kuma ci tarar hukumar kwallon kafa ta Ƙasar Moroko (FRMF) dala 200,000, saboda rashin da’ar ‘yan wasan a filin wasa a lokacin wasan karshe na kofin kasashen Afirka AFCON 2025.

Da kuma karin tarar dala 100,000 saboda rashin da’a na ‘yan wasanta da ma’aikatan horaswa, waɗanda suka mamaye duba VAR suka kuma hana aikin alkalin wasa, wanda ya saɓa wa ƙa’idodin yin wasa sashe na 82 da 83 na Dokar Ladabtarwa ta CAF.

A kwai kuma tarar da aka ci Hukumar Kwallon Kafa ta Moroko (FRMF) dala 15,000 saboda amfani da na’urorin laser da magoya bayanta suka yi a lokacin wasan aikata haka laifine.

Dangane da korafin kan Hukumar Kwallon Kafa ta Moroko (FRMF) ta shigar kan zargin keta dokoki daga Hukumar Kwallon Kafa ta Senegal (FSF) inda ta bukace a kwace kofin bisa sashe na 82 da 84 na Dokokin Gasar Cin Kofin Afirka kuwa

hukumar Ladabtarwa ta CAF ta yi watsi da wannan korafin da Hukumar Kwallon Kafa Moroko (FRMF) ta shigar kan Senegal (FSF).

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Wasanni

Post navigation

Previous Post: Maganganun Jami’an Shige Da Fice Dana Shugaban Kasa Trump Suna Cin Karo Da Juna
Next Post: Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Biyan Hakkokin Tsofin Ma’aikata 800

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Zuwa Jami’ar Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Allah Ya Yi Wa Sheikh Dahiru Bauchi Rasuwa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai
Wikki Tourists FC: Ta Yi Sabbin ‘Yan Wasa Uku Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamna Inuwa Yahaya ya Rusa Majalisar Zantaswa ta Jihar Gombe Labarai
  • Na Yi Murabus Ne Don Amurka Ta Keta Haddin Iraniyawa Amurka
  • Iran Zata Kawo Karshen Yaki Da Isra’ila Da Amurka Amurka
  • An Farmaki ‘Yan Bindiga Da Dama A Jihar Zamfara Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Isa Legas Domin Hutun Karshen Shekara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hukumar NDLEA Ta Kama Wata Mata Da cikin Bogi Na ƙwaya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Janet Ce Gwarzuwar ‘Yar Wasan Mako NWFL Wasanni
  • Dakarun Tsaron Ruwan Amurka Sunfara Killace Hanyoyi Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.