Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Biyan Hakkokin Tsofin Ma’aikata 800
Published: January 29, 2026 at 9:37 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Kebbi Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu), ya amince da biyan kudaden garatuti da tallafin rasuwa ga ma’aikatan gwamnati da suka yi ritaya da kuma wadanda suka rasu, da ma’aikatan kwantiragi, ma’aikatan kananan hukumomi da kuma na Hukumar Ilimin Kananan Hukumomi.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Shugaban Ma’aikatan jihar Malami Shekare mni, ya fitar wadda Daraktan Gudanarwa, Rashidu Muhammad Bala FCIA, FCIHRSM, ya sanya wa hannu.

Sanarwar ta bayyana cewa amincewar ta shafi kashi biyu na biyan kudaden.

Kashi na farko ya shafi daga 16 ga watan Maris zuwa 15 ga Yuni, 2025, inda aka biya jimillar kudi Naira ₦933,028,860.33 ga mutum 404.

Kashi na biyu kuwa ya shafi daga 16 ga Yuni zuwa 15 ga Satumba, 2025, inda aka biya jimillar kudi Naira ₦932,948,801.39 ga mutane 443.

Biyan wadannan hakkoki na nuna jajircewar gwamnatin Nasir Idris wajen kula da walwalar ma’aikata da iyalan wadanda suka rasu, tare da kudurinta na rage basussukan da ake bin gwamnati a bangaren ayyuka.

Labarai

Post navigation

Previous Post: CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025
Next Post: Majalisar Dottawa Ta Kafa Komitin Dokar Zabe

Karin Labarai Masu Alaka

Isra’ila Tace Bazata Sake Kai Hari Kan Cibiyar Gas Ta Iran Ba Afrika
Gwamnatin Kasar Ghana Ta Rage Farashin Cocoa Afrika
Zanga-Zangar Adawa Da Harin Amurka Da Isra’ila Ya Zamo Tarzoma A Pakistani Afrika
Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
Hawan Durba A Fadar Sarkin Zazzau Afrika
Samar Da Albarkatun Mai Ya Ragu A Iraq Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Kasar Ukraine Yace Rasha Tana Bawa Iran Bayanan Sirri Afrika
  • EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro
  • Yanbindiga sun Kashe mutun guda tare da yin garkuwa da mutane kimanin 100 a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
  • AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya Wasanni
  • Guguwa Mai Karfi Ta Raunata Dubban Mutane A Madagascar Labarai
  • Gwamnatin Gombe Ta Dauki Sabbin Matakan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • CNG Ta Farfado Da Jarin Masu Adaidaita Sahu A Kaduna Afrika
  • An Kashe Falatsinawa Biyar A Wani Hari Da Isra’ila Takai Wata Makaranta A Gaza Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.