Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Shugaban Kasar Amurka Yakara Hana Wasu Kasashe Shiga Amurka Ciki Harda Nijar
Published: December 17, 2025 at 3:22 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Donald Trump na Amurka ya kara wasu kasashe 7 cikin kasashen da gwamnatinsa zata haramta ma ‘yan kasar shiga kasar Amurka, cikinsu har da ‘yan Jamhuriyar Nijar.

Fadar White House ta fada ranar talata cewa, shugaba Trump ya sanya hannu a kan wata takardar sanarwa ta karawa da karfafa jerin kasashen da za a sanya ma al’ummarsu takunkumin shiga Amurka a saboda tabbatar da cewa ba su bincika ko bayar da bayanai ga hukumomin Amurka ta yadda zasu iya kare tsaron kasa daga irin wadannan mutane da zasu shigo kasa daga wadannan wurare.

Wannan matakin na ranar talata, a bayan haramta ma ‘yan Jamhuriyar Nijar shigowa Amurka, zai kuma kara da ‘yan kasashen Burkina Faso, Mali, Sudan ta Kudu, Sham ko Syria, da kuma wadanda suke rike da takardun tafiye-tafiye na hukumar mulkin Falasdinu.

Har ila yau wannan matakin yanzu ya haramta shigowar dukkan ‘yan kasashen Saliyo da Laos, wadanda a baya an takaita shigowarsu ne kawai.

Wannan sabon haramcin zai fara aiki daga ranar 1 ga wata mai zuwa na Janairu.

Sanya kasar Sham cikin jerin kasashen na zuwa ne duk da alkawarin da Trump yayi na cewa zai yi duk bakin kokarinsa na ganin kasar ta samu nasarar shawo kan matsalolinta a bayan tattaunawar da yayi da shugaban kasar, Ahmed al-Sharaa, wanda a can baya kwamanda ne na kungiyar al Qaida wanda Amurka ta taba sa takunkumi a kansa.

Fadar White House ta gabatar da hujjar cewa mutanen kasar Sham da suke shigowa Amurka suna ci gaba da zama har bayan karewar takardun bizar su, tana mai cewa dalilinta na daukar wannan matakin a kan Sham ke nan.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Kungiyar Kwadago Ta NLC Ta Gudanar Da Zanga-Zanga Bisa Matsalar Tsaro
Next Post: Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa

Karin Labarai Masu Alaka

Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke Amurka
Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka
Dillalan Mai Suna Fuskantar Karancin Mai Sakamakon Yakin Amurka Da Iran Afrika
Rundunar Sojin Iran Tace Harin Amurka Ya Kashe Musu Sama Da Mutane Dari Afrika
Amurka Da Iran Sun Cimma Yarjejeniya Tsagaita Wuta Na Makonni Afrika
Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai
  • Tsohon Jagoran Masu Kishin Kasa A Hungry Ya Amince Da Shan Kaye Labarai
  • Anyi Bikin Cikar Tsohon Shugaban Kasa Abdulsalami Shekaru 84 Afrika
  • Rikici Tsakanin NNPC Da Kungiyar Gwamnoni Akan Gibin Kudade Labarai
  • A Hudubar Kirsimeti Paparoma Leo Ya Jajantawa Al’ummar Falatsinu A Yankin Zirin Gaza Amurka
  • Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
  • A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela Amurka
  • Shirin Manuniya Yau Juma’a 12.12.2026 Shirye-Shirye
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.