Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Inuwa Ya Bukaci A Kara Zuba Jari A Ilimin Sana’o’i Domin Samar Wa Matasa Aikin Yi Afrika
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar Bamanga Tukur, Sun Yaba Da Gudunmawarsa Ga Najeriya Afrika
  • Tsohon Shugaban PDP, Bamanga Tukur, Ya Rasu Yana da Shekaru 91 Afrika
  • Filato: Gwamnati Ta Ƙarfafa Matakan Kariya Yayin Sake Buɗe Makarantu Afrika
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika

Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne
Published: December 16, 2025 at 8:44 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan sandan kasar Australiya sun ce ‘yan bindiga biyu da ake zargin sun kai harin da ya kashe mutane 15 lokacin wani biki na Yahudawa a Bondi Beach dake birnin Sydney, sun yi tattaki zuwa kasar Philippines kafin harin, kuma da alamun masu kaunar akida irinta ISIS ce.

‘Yan sandan sun fada yau talata cewa Sajid Akram mai shekaru 50 wanda kuma aka kashe a wurin, da dansa Naveed Akram, mai shekaru 24 da haihuwa wanda shi ma aka harba amma yana kwance a asibiti, sun tafi kasar Philippines a watan da ya shige, kuma ana bincike abinda ya kai su.

Jami’an kula da shige da ficen baki na Philippines sun ce mutanen biyu sun je Manila babban birnin kasar suka wuce Davao a kudancin kasar daga ranar 1 zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba da suka baro can, makonni kadan klafin harbe-harben na Bondi.

Uban ya je shi Philippines dauke da Fasfo na kasar Indiya, shi kuma dan da fasfo na Australiya.

Hukumomi suka ce babu wata shaida da ta nuna wata alaka a tsakaninsu da wata kungiyar ta’addanci ko kuma sa mun horo daga ire-iren su.

Wani musulmi magidanci mai suna Ahmed al Ahmed da ake yaba masa a zaman gwarzo a bayan da yayi kukan kura ya abka kan daya daga cikin ‘yan bindigar, sannan yana kwance a asibiti a Sydney yana jinyar harbinsa da aka yi har sau hudu.

Shugabannin Australiya da ma shugaba Donald Trump na Amurka suna yaba ma Ahmed a zaman gwarzo.

Asusun da aka kafa na nema masa gudumawar kudin jinya a yanzu ya tara fiye da Dala miliyan 1 da dubu 260.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya!
Next Post: Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Maganganun Jami’an Shige Da Fice Dana Shugaban Kasa Trump Suna Cin Karo Da Juna Amurka
‘Yan Sanda Sunce Mutum Daya Ne Yakai Hare-Haren Jami’ar Brown Da Kuma Na MIT Boston Amurka
‘Yan Sandan Birnin New York Sun Karyata Zargin Jefa Bom Ga Masu Zanga Zanga Amurka
Amurka Zatayi Amfani Da Sansanonin Birtaniya Amurka
‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
An Kama Tsohon Jakadan Birtaniya A Amurka Peter Mandelson Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Inuwa Ya Bukaci A Kara Zuba Jari A Ilimin Sana’o’i Domin Samar Wa Matasa Aikin Yi
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar Bamanga Tukur, Sun Yaba Da Gudunmawarsa Ga Najeriya
  • Tsohon Shugaban PDP, Bamanga Tukur, Ya Rasu Yana da Shekaru 91
  • Filato: Gwamnati Ta Ƙarfafa Matakan Kariya Yayin Sake Buɗe Makarantu
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tashoshin Mai Basa Iya Loda Mai A Rasha Labarai
  • Yakin Iran Da Isra’ila Da Amurka Zai Shafi Kasashen Afirka – Masana Afrika
  • Rikici Ya Lafa A Kasar Iran Bayan Daukar Matakai Labarai
  • Babban Bankin Najeriya Ya Rage Kudin Ruwa Da Kashi Daya Cikin Dari Labarai
  • Gwamnatin Tinubu Ta Karyata Kafa Kamfanin Gwal A Legas Labarai
  • Iran Zata Mayarwa Amurka Martani Amurka
  • Gwamnatin Sokoto Tabada Umarnin Biyan Albashin Watan Fabrairu Labarai
  • Mayakan Houthi Zasu Shiga Yakin Amurka Da Isra’ila Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.