Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne
Published: December 16, 2025 at 8:44 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan sandan kasar Australiya sun ce ‘yan bindiga biyu da ake zargin sun kai harin da ya kashe mutane 15 lokacin wani biki na Yahudawa a Bondi Beach dake birnin Sydney, sun yi tattaki zuwa kasar Philippines kafin harin, kuma da alamun masu kaunar akida irinta ISIS ce.

‘Yan sandan sun fada yau talata cewa Sajid Akram mai shekaru 50 wanda kuma aka kashe a wurin, da dansa Naveed Akram, mai shekaru 24 da haihuwa wanda shi ma aka harba amma yana kwance a asibiti, sun tafi kasar Philippines a watan da ya shige, kuma ana bincike abinda ya kai su.

Jami’an kula da shige da ficen baki na Philippines sun ce mutanen biyu sun je Manila babban birnin kasar suka wuce Davao a kudancin kasar daga ranar 1 zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba da suka baro can, makonni kadan klafin harbe-harben na Bondi.

Uban ya je shi Philippines dauke da Fasfo na kasar Indiya, shi kuma dan da fasfo na Australiya.

Hukumomi suka ce babu wata shaida da ta nuna wata alaka a tsakaninsu da wata kungiyar ta’addanci ko kuma sa mun horo daga ire-iren su.

Wani musulmi magidanci mai suna Ahmed al Ahmed da ake yaba masa a zaman gwarzo a bayan da yayi kukan kura ya abka kan daya daga cikin ‘yan bindigar, sannan yana kwance a asibiti a Sydney yana jinyar harbinsa da aka yi har sau hudu.

Shugabannin Australiya da ma shugaba Donald Trump na Amurka suna yaba ma Ahmed a zaman gwarzo.

Asusun da aka kafa na nema masa gudumawar kudin jinya a yanzu ya tara fiye da Dala miliyan 1 da dubu 260.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya!
Next Post: Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Rundunar Sojin Amurka Sunfara Ficewa Daga Kasar Sham Amurka
Amurka Zata Hana Kwankwaso Shiga Kasar Amurka
Kasar Afirka Ta Kudu Ta Tsare Wasu Amurkawa Amurka
Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
Kasar Rasha Ta Zargi Ukraine Da Kai Hari Gidan Shugaban Rasha Amurka
An Yi Fashin Kaguwa Da Dodon-Kodi Na Miliyoyin Dalar Amurka Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Jam’iyyar APC Ta Rantsar Da Sabbin Shugabanni a Jihar Neja Labarai
  • Rasha Da Ukraine Sun Cigaba Da Yakar Juna Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya kori Wasu Hadimansa Bisa Cin Zarafin Kansila Najeriya
  • Afirka Ta Kudu Da Kenya Sun Bayyana Yaudarar ‘Yan Kasashe Da Yawa Tare Da Sakasu Yaki Labarai
  • Kasar Morocco Ta Kwashe ‘Yan Kasar Daga Sassan Ambaliyar Ruwa Afrika
  • Akwai Nasara A Tattaunawar Da Akeyi Tsakanin Iran Da Amurka Afrika
  • Ankara Gano Wani Abu Mai Kama Da Abun Fashewa A Jabo Jihar Sokoto Tsaro
  • Shirin: Lafiya Jari Ce 11.21.25 Kiwon Lafiya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.