Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Ana Zargin Cewa ‘Yan Bindiga Biyun Nan Mambobin Kungiyar ISIS Ne
Published: December 16, 2025 at 8:44 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan sandan kasar Australiya sun ce ‘yan bindiga biyu da ake zargin sun kai harin da ya kashe mutane 15 lokacin wani biki na Yahudawa a Bondi Beach dake birnin Sydney, sun yi tattaki zuwa kasar Philippines kafin harin, kuma da alamun masu kaunar akida irinta ISIS ce.

‘Yan sandan sun fada yau talata cewa Sajid Akram mai shekaru 50 wanda kuma aka kashe a wurin, da dansa Naveed Akram, mai shekaru 24 da haihuwa wanda shi ma aka harba amma yana kwance a asibiti, sun tafi kasar Philippines a watan da ya shige, kuma ana bincike abinda ya kai su.

Jami’an kula da shige da ficen baki na Philippines sun ce mutanen biyu sun je Manila babban birnin kasar suka wuce Davao a kudancin kasar daga ranar 1 zuwa ranar 28 ga watan Nuwamba da suka baro can, makonni kadan klafin harbe-harben na Bondi.

Uban ya je shi Philippines dauke da Fasfo na kasar Indiya, shi kuma dan da fasfo na Australiya.

Hukumomi suka ce babu wata shaida da ta nuna wata alaka a tsakaninsu da wata kungiyar ta’addanci ko kuma sa mun horo daga ire-iren su.

Wani musulmi magidanci mai suna Ahmed al Ahmed da ake yaba masa a zaman gwarzo a bayan da yayi kukan kura ya abka kan daya daga cikin ‘yan bindigar, sannan yana kwance a asibiti a Sydney yana jinyar harbinsa da aka yi har sau hudu.

Shugabannin Australiya da ma shugaba Donald Trump na Amurka suna yaba ma Ahmed a zaman gwarzo.

Asusun da aka kafa na nema masa gudumawar kudin jinya a yanzu ya tara fiye da Dala miliyan 1 da dubu 260.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya!
Next Post: Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Trump Yace Babu Maganar Kawo Karshen Yakin Amurka Da Iran Amurka
Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
Amurka Da Kasashen Yamma Suna Cigaba Da Kai Ruwa Rana Akan Nukiliyar Iran Afrika
Shugaba Trump Yayi Barazanar Tarwatsa Cibiyar Makamashin Iran Amurka
Wasu Kasashen Turai Zasu Daina Tura Sojinsu Wata Cibiyar Sojojin Amurka Amurka
Kasashen Amurka Da China Sun Matsawa Ghana Domin Rage Kudaden Haraji Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Arsenal Ta Fara Kare Kambun Gasar Premier League Da Ci 3-0 A Kan Coventry City Wasanni
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025. Wasanni
  • Jirgin Sojojin Ruwa Yayi Gobara A Cross River Najeriya
  • UNICEF Ta Tallafawa Jihar Bauchi Da Babura Afrika
  • Shugaban Kasar Brazil: Yakamata Amurka Ta Gurfanar Da Shugaban Venezuela A Kotu Afrika
  • Libya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashen Faransa Da Amurka Afrika
  • Ganduje Ne Yasa Aka Kama Ni Inji Muhuyi Magaji Najeriya
  • Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.