Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

Kasar Malawi Ta Kaddamar Da Rigakafin Shan Inna
Published: February 14, 2026 at 7:29 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A ranar Laraban da ta gabata ne kasar Malawi ta fara yiwa yara allurar rigakafin shan Inna, inda ma’aikatan lafiya ke bi ajujuwan makaranta suna diga wa yara maganin rigakafin a bakin su, da zata kare su daga cutar shan Inna.

Wannan na nuna cewa har yanzu ba’a kawar da cutar a duniya ba, wadda yawanci take kama yara, kuma tana iya jayo shanyewar jiki, duk da kokarin da Hukumar Lafiya ta Duniya tare da ‘yan hadin guiwa suka shafe shekaru 35 suna yi.

Jami’an kiwon lafiya sun amince cewa sau da dama sun yi kokarin zuwa gab da kawar da cutar, ciki har da a shekaru 5 da suka wuce, inda masu dauke da cutar 5 kacal aka samu a duniya.

Amma hukumar lafiya ta Duniya ta ce an Samu masu dauke da cutar 38 tsakanin watan Janairu zuwa watan Octobar shekara ta 2025, dukkan su kuma a kasashen Pakistan da Afghanistan, da kuma wasu 151 da allurar rigakafin shan inna ta haddasa musu cutar a kasashe 13.

Kiwon Lafiya, Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Amurka Zata Aika Jiragen Yaki Biyu Gabas Ta Tsakiya
Next Post: An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi

Karin Labarai Masu Alaka

Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar Amurka
Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Bukaci Musulmi Su Rungumi Tausayi Da Ƙaunar Juna Afrika
Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika
Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai
Adamu: “Yakar Cin Hanci Daga Tushe Itace Mafita Daya Tilo” Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Tace Zata Gama Yakin Iran Cikin Makonni Afrika
  • Manchester United Ta Sallami Ruben Amorim Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda Afrika
  • Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe Afrika
  • Babu Dabbar Da Zata Sake Shiga Amurka Daga Mexico! Amurka
  • Harin Bom Din Maiduguri Ya Kashe Mutane Biyar Ya Raunata Fiye Da Talatin Najeriya
  • Wata Kotu A Abuja Ta Wanke Abba Kyari Afrika
  • Shirin Manuniya Yau Juma’a 12.12.2026 Shirye-Shirye
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.