Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Inuwa Ya Bukaci A Kara Zuba Jari A Ilimin Sana’o’i Domin Samar Wa Matasa Aikin Yi Afrika
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar Bamanga Tukur, Sun Yaba Da Gudunmawarsa Ga Najeriya Afrika
  • Tsohon Shugaban PDP, Bamanga Tukur, Ya Rasu Yana da Shekaru 91 Afrika
  • Filato: Gwamnati Ta Ƙarfafa Matakan Kariya Yayin Sake Buɗe Makarantu Afrika
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika

Tsohon Lauyan Amurka Jack Smith Ya Fadi Maganganu Game Da Donald Trump
Published: January 23, 2026 at 2:20 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Tsohon lauyan Amurka Jack Smith wanda bai sami nasarar ci gaba da gurfanar da Trump gaban shari’a ba saboda zaben sa da aka yi, ya gayawa kwamitin majaisar wakilan Amurka ranar Alhamis cewa, Trump ya “nemi hanyoyin yin tazarce,” duk da cewa ya fadi zabe a shekara ta 2020, yayinda yake amsa zargen zargen da ‘yan Republican suke yi masa game da binciken da ya gudanar kan Donald Trump.

Jack Smith ya amsa tambayoyi daga kwamitin kula da harkokin shari’a karkashin ‘Yan Republican, kan kararraki biyu da ya shigar gaban kotu yana tuhumar Trump da laifin neman ci gaba da mulki alhali ya fadi zabe, da kuma murdiya kan muhimman kasidun gwamnati kana daga bisani yayi watsi da su bayan Trump ya sami nasara a zaben da aka yi bara.

Wannan shine karo na farko da Amurkawa za su ji daga bakin Smith kai tsaye kan wadannan shari’u biyu da suka mamaye harkokin Trump bayan ya sauka daga mulki.

“An tuhumi Trump ne saboda shaida ta tabbatar da gangan, ya karya dokokin da yasha rantsuwa zai kare,” Smith ya gayawa wakilan majalisa dake kwamitin. Ya ci gaba da cewa idan aka buka ce ni in jagoaranci shar’iar tsohon shugaban Amurka da shaidar da ake ita, zan yi haka ba tare da bata lokaci, ko la’akari daga wace jam’iyya ya fito ba.

Lauya Smith yace yana jin ma’aikatar shari’a ta Amurka zata shigar da kara a gaban kotu akansa, sakamkon binicken da yayi kan shugaba Trump.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Shugaban Rasha Yafara Ganawa Da Jakadun Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Ukraine
Next Post: Gwamnan Jihar Kano Ya Fice Daga Jam’iyar NNPP

Karin Labarai Masu Alaka

Dubban ‘Yan Gudun Hijira Sun Halaka Amurka
Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Sojojin Amurka Sun Kashe Wasu Fararen Hula Ba Dalili Amurka
Shugaban Kasar Faransa Ya Zanta Da Shugaban Kasar Iran Afrika
Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
Shugaba Donald Trump Ya Bayyana Cewa Yana Cikin Masu Zaben Sabon Jagoran Iran Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Inuwa Ya Bukaci A Kara Zuba Jari A Ilimin Sana’o’i Domin Samar Wa Matasa Aikin Yi
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar Bamanga Tukur, Sun Yaba Da Gudunmawarsa Ga Najeriya
  • Tsohon Shugaban PDP, Bamanga Tukur, Ya Rasu Yana da Shekaru 91
  • Filato: Gwamnati Ta Ƙarfafa Matakan Kariya Yayin Sake Buɗe Makarantu
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Ceto Wasu Daliban St. Mary’s Tsaro
  • Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Yayi Ajalin ‘Yan Ghana 50 Afrika
  • Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya Kiwon Lafiya
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
  • Sakamakon Yakin Gabas Ta Tsakiya Kowacce Gangar Mai Ta Haura Dala 100 Afrika
  • Dillalan Mai Suna Fuskantar Karancin Mai Sakamakon Yakin Amurka Da Iran Afrika
  • Hukumar IMF Tana Naziri Domin Kara Bada Lamuni Ga Kasar Zambiya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.