Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya taya Alhaji Murtala Sule Garo murnar rantsar da shi a matsayin sabon Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, wanda Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kaddamar a ranar Talata.
Gwamna Abba ya nada Murtala Garo ne domin cike gurbin da Comrade Aminu Abdulsalam ya bari, bayan murabus din da ya yi biyo bayan sauya shekar gwamnan zuwa jam’iyyar APC.
Murtala Garo, mai shekara 48, gogajen dan siyasa ne wanda ya rike mukamai daban-daban, ciki har da Shugaban Karamar Hukumar Kabo,Kwamishinan Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Al’amuran Masarautu a karkashin gwamnatin tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, kuma dan takarar Mataimakin Gwamna na jam’iyyar APC a zaben shekarar 2023.
Shugaba Tinubu ya jinjina wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa wannan nadi, yana mai bayyana cewa matakin zai karfafa hadin kan da ake bukata a cikin sahu da jerin mambobin jam’iyyar APC a Jihar Kano.
Haka zalika, Shugaban ya yi kira ga daukacin masu ruwa da tsaki da su mara wa Gwamnan da mataimakinsa baya domin ciyar da jihar gaba.
Ya kuma bukaci sabon Mataimakin Gwamnan da ya yi aiki kafada-da-kafada da gwamna domin samar da shugabanci na gari da zai bunkasa jihar.
A karshe, Shugaba Tinubu ya yi wa Murtala Garo fatan alheri a wannan sabon nauyi da aka dora masa.


