Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa Afrika
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
  • Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane Afrika
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Afrika
  • Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Ya Rasu A Abuja Bayan Doguwar Jinya Afrika

Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci
Published: April 27, 2026 at 10:26 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Yayin da shirye-shiryen babban zaɓen shekarar 2027 ke ƙara ƙarfi a Jihar Gombe, ƙungiyoyin fararen hula sun yi kira ga jam’iyyun siyasa da su ƙara ba mata dama a harkokin siyasa.

Ƙungiyar Gombe Network of Civil Society Organizations, GONET, tare da Gombe Women Agenda, GWA, sun buƙaci jam’iyyun siyasa su nuna ƙuduri wajen haɗa mata ta hanyar aiwatar da tsarin fifikon mata (affirmative action) da kuma goyon bayan samar da kujeru na musamman ga mata.

A cikin wata sanarwar haɗin gwiwa da Ibrahim Yusuf da Dakta Leah Iliya Jalo suka sanya wa hannu a madadin GONET, ƙungiyoyin sun bayyana damuwa kan yadda har yanzu mata ke ƙarƙashin wakilci a muƙaman jagoranci da yanke shawara a jihar, duk da irin gagarumar gudunmawar da suke bayarwa ga ci gaban al’umma da kuma kusan daidaiton yawan su da maza.

Sanarwar ta danganta wannan gibi ba da ƙarancin ƙwarewa ko sha’awar mata ba, sai dai ga tsauraran matsalolin tsari, al’adu da kuma na kuɗi da ke cikin tsarin siyasa da jam’iyyu, waɗanda ke hana mata shiga harkokin siyasa yadda ya kamata.

Ƙungiyoyin sun jaddada cewa tsarin fifikon mata da kujerun musamman bai kamata a ɗauke su a matsayin wata gata ba, sai dai a matsayin matakan gyara domin kawar da tsofaffin rashin adalci da kuma tabbatar da shugabanci mai haɗa kowa da kowa.

Sun kuma ce ingantacciyar dimokuraɗiyya dole ne ta wakilci bambancin jama’a, tare da gargadin cewa ware mata daga jagoranci na rage ingancin shugabanci da kuma tauye ci gaba.

Daga ƙarshe, sun buƙaci jam’iyyun siyasa da su ɗauki matakai na musamman, ciki har da aiwatar da dokokin fifiko ga mata, amincewa da kudirin kujerun musamman ga mata, ware kaso mai tsoka na tikitin takara ga mata, rage ko soke kuɗin fom ɗin takara, da kuma samar da tsare tsaren tallafi kamar horo da kariya daga tashin hankali na siyasa.

Sun kuma yi kira ga shugabannin jam’iyyu da masu ruwa da tsaki da su ɗauki mataki cikin gaggawa, suna mai cewa zaɓen 2027 wata muhimmiyar dama ce ta inganta daidaito tsakanin jinsi da kuma ƙarfafa dimokuraɗiyya a Jihar Gombe.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: NAHCON Ta Kaddamar da Tawagar Malamai
Next Post: Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci

Karin Labarai Masu Alaka

Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Labarai
Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai
Kotu A Kasar Uganda Ta Bada Belin ‘Yar Gwagwarmaya Afrika
Shugaba Tinubu Ya Tafi Kasar Faransa Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Samar Da Wuta Mai Aiki Da Hasken Rana A Jami’ar ADUSTECH Afrika
Kasar Habasha Da Turkiyya Sun Kulla Yarjejeniyar Makamashi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar Raya Birane Ta Rushe Gine-Ginen Da Suka Keta Dokokin Tsara Birane A Gombe
  • Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa
  • Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Zargin Tauye Ka’idojin Zabe: Malam Pantami Ya Janye Daga Takara Afrika
  • Shugaban Amurka Zai Sake Gine Gaza Amurka
  • Gwamnatin Najeriya Ta Taya Super Eagles Murnar Lashe Tagulla A Gasar AFCON Wasanni
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Masu Zuba Jari A Birnin Paris Afrika
  • ‘Yan Jarida Sunyi Mummunan Hatsari A Bauchi Labarai
  • Kasar Aljeriya Ta Soke Yarjejeniyar Jirgin Sama Tsakaninta Da Daular Larabawa Labarai
  • An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
  • Amurka Ta Kai ‘Yan Cirani Kamaru Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.