Kasar Tukiya da kasar Habasha sun rattaba hannun kan yarjejeniyar fahimta na hadin guiwa kan makamashi a yayin wata ziyara da shugaban Turkiyya, Racep Tayyib Erdogan ya kai Addis Ababa, babban birnin kasar Habasha ranar Talata, a cewar ma’aikatar makamashi ta Turkiya, inda yarjejeniyar zata kai ga hadaka wajen samarwa da kuma ayyukan makamashin.
Erdogan ya kai ziyarar kwana daya ne, bayan da prime ministan Habasha Abiy Ahmed ya gayyace shi. Wannan ita ce gayya ta farko zuwa kasar cikin shekaru 11.
Kasashen biyu sun rattaba hannu a yarjejeniyar ne a wani biki da aka gudanar bayan tattaunawa tsakanin shugabannin biyu. Ministan makamashi na Turkiya ya ce wannan hanya ce da zata karfafa hadin kai.


