Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya
Published: March 13, 2026 at 5:12 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya

Daga Adamu Aliyu Ngulde, Maiduguri

An gargaɗi mazauna birnin Maiduguri da su guji wallafawa da kuma yaɗa labaran ƙarya a kafofin sadarwar zamani domin kauce wa haifar da tashin hankali a cikin al’umma.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Borno, ASP Nahum Kenneth Daso, ya musanta rahotannin da ke yawo a kafofin sadarwar zamani da ke cewa an samu wani abu da ake kyautata zaton abin fashewa ne a harabar wani masallaci da ke unguwar Abuja Sheraton a Maiduguri.

Ya ce, “Wannan labari ba shi da tushe balle makama, domin babu wani abin fashewa da jami’an tsaro suka samu wanda zai zama barazana ga zaman lafiyar al’umma.”

Hakazalika, ya yi gargaɗin cewa, “Yaɗa bayanai marasa tushe na iya sanya mazauna birnin Maiduguri cikin firgici tare da kawo cikas ga ƙoƙarin hukumomin tsaro na tabbatar da zaman lafiya a tsakanin al’umma.”

A cewarsa, “Ya kamata jama’a su riƙa tabbatar da sahihancin labarai daga amintattun majiyoyi kafin su yaɗa su a kafofin sadarwar zamani.”

Shi ma Malam Bukar Abubakar ya ce, “Akwai buƙatar jama’a su tsaftace yadda suke amfani da kafofin sadarwa domin kauce wa haddasa husuma a cikin al’umma.”

Wasu mazauna birnin, ciki har da Mathew Joshua da Ahmed Mahmud, sun ce, “Duk da matsalolin tsaro da ke addabar wasu sassan jihar, akwai buƙatar jama’a su kwantar da hankalinsu tare da gujewa yaɗa rahotannin da ba a tabbatar da su ba, waɗanda ka iya ƙara dagula zaman lafiya a Maiduguri.”

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Trump Tana Cigaba Da Korar Baki Daga Amurka
Next Post: Yunkurin Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi Na Kara Kankama A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati Labarai
Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Rikicin Gabas Ta Tsakiya Yanuna Alakar Kasashen Da Najeriya Afrika
Mutum Mafi Tsufa A Saudiyya Ya Rasu Yana Da Shekaru 142 Labarai
Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan Labarai
Kyautata Dangantaka Tsakanin Jami’an Tsaro Da Al’umma Ce Mafita Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Ƙasar Djibouti Ya Sake Lashe Zaben Shugaban Kasar Afrika
  • Jagoran Adawar Uganda Bobi Wine Ya Fice Daga Kasar Afrika
  • Sakataren Kungiyar NATO Yayi Magana Da Hukumomin Kasashe Afrika
  • Hukumar IMF Tana Naziri Domin Kara Bada Lamuni Ga Kasar Zambiya Afrika
  • Angano Gawar Wani Dan Myanmar A Arewacin New York Afrika
  • Kotu A Birnin Tarayya Abuja Ta Bada Belin Tsohon Minista Abubakar Malami Najeriya
  • Yan Najeriya na ci gaba da maida martani akan sabuwar dokar zabe da majalisar Dattawan kasar ta Amince dashi Najeriya
  • Kungiyar Kiristoci Ta Wanke Gwamnan Bauchi Daga Zargin Ta’addanci Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.