Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya
Published: March 13, 2026 at 5:12 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya

Daga Adamu Aliyu Ngulde, Maiduguri

An gargaɗi mazauna birnin Maiduguri da su guji wallafawa da kuma yaɗa labaran ƙarya a kafofin sadarwar zamani domin kauce wa haifar da tashin hankali a cikin al’umma.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Borno, ASP Nahum Kenneth Daso, ya musanta rahotannin da ke yawo a kafofin sadarwar zamani da ke cewa an samu wani abu da ake kyautata zaton abin fashewa ne a harabar wani masallaci da ke unguwar Abuja Sheraton a Maiduguri.

Ya ce, “Wannan labari ba shi da tushe balle makama, domin babu wani abin fashewa da jami’an tsaro suka samu wanda zai zama barazana ga zaman lafiyar al’umma.”

Hakazalika, ya yi gargaɗin cewa, “Yaɗa bayanai marasa tushe na iya sanya mazauna birnin Maiduguri cikin firgici tare da kawo cikas ga ƙoƙarin hukumomin tsaro na tabbatar da zaman lafiya a tsakanin al’umma.”

A cewarsa, “Ya kamata jama’a su riƙa tabbatar da sahihancin labarai daga amintattun majiyoyi kafin su yaɗa su a kafofin sadarwar zamani.”

Shi ma Malam Bukar Abubakar ya ce, “Akwai buƙatar jama’a su tsaftace yadda suke amfani da kafofin sadarwa domin kauce wa haddasa husuma a cikin al’umma.”

Wasu mazauna birnin, ciki har da Mathew Joshua da Ahmed Mahmud, sun ce, “Duk da matsalolin tsaro da ke addabar wasu sassan jihar, akwai buƙatar jama’a su kwantar da hankalinsu tare da gujewa yaɗa rahotannin da ba a tabbatar da su ba, waɗanda ka iya ƙara dagula zaman lafiya a Maiduguri.”

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Trump Tana Cigaba Da Korar Baki Daga Amurka
Next Post: Yunkurin Samar Da ‘Yan Sandan Jihohi Na Kara Kankama A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

NITDA Da GOSIDEC Sun Horar Da Ma’aikatan Gombe Don Inganta Ayyukan Gwamnati Afrika
Amurka Zata Saidawa Saudiyya Da Jirgin Yaki Samfurin F35 Labarai
Kasar Masar Ta Dakatar Da Wasu Ayyukan Da Ake Amfani Da Man Fetur Da Diesel Labarai
Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin Afrika
Ukraine Ta Tura Tawagar Kwarerru Zuwa Kasashen Larabawan Domin Basu Kariya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato Afrika
  • Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026 Labarai
  • Gwamna Inuwa Yahaya ya Rusa Majalisar Zantaswa ta Jihar Gombe Labarai
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Kotun Uganda Tayi Watsi Da Karar Hukumomin Kasar Afrika
  • Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland Wasanni
  • Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ghana Tayi Watsi Da Yarjejeniya Akan Hakar Ma’adanai Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.