Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi
Published: December 23, 2025 at 3:32 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ƙananan hukumomi na neman karɓar kuɗaɗensu kai tsaye yayin da jihohi suka riƙe N7.43tn

Ƙungiyar Shugabannin Ƙananan Hukumomi ta Najeriya (ALGON) da Ƙungiyar Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi ta Ƙasa (NULGE) sun bayyana cikakken goyon bayan su ga shirin Shugaba Bola Tinubu na tabbatar da biyan kuɗaɗen ƙananan hukumomi kai tsaye daga Asusun Tarayya (FAAC), duk da cewa gwamnatocin jihohi na ci gaba da riƙe iko kan rarraba kuɗaɗen ƙananan hukumomi.

A yayin taron kwamitin zartarwa na ƙasa karo na 15 na jam’iyyar APC da aka gudanar a Babban Dakin Taro na Fadar Shugaban Ƙasa a Abuja, Tinubu ya bukaci gwamnonin jihohi su mutunta hukuncin Kotun Ƙoli da ya ba wa ƙananan hukumomi ‘yancin cin gashin kan su ta fuskar kuɗi.

Shugaban ya yi gargaɗin cewa idan gwamnonin suka ƙi bin hukuncin, zai iya fitar da umarnin shugaban ƙasa (Executive Order) domin tabbatar da cewa ana tura kuɗaɗen ƙananan hukumomi kai tsaye daga FAAC zuwa asusun su.

Wannan jawabi na Tinubu ya biyo bayan hukuncin Kotun Ƙoli na ranar 11 ga Yuli, 2024, wanda ya goyi bayan ƙarar da Gwamnatin Tarayya ta shigar domin tilasta ‘yancin kuɗi ga ƙananan hukumomi.

A hukunci ɗaya tilo, kwamitin alkalai bakwai na Kotun Ƙoli ya ayyana cewa ba a bisa doka ba ne gwamnatocin jihohi ke riƙe ko sarrafa kuɗaɗen da aka ware wa ƙananan hukumomi.

Kotun ta kuma ce kafa kwamitocin rikon ƙwarya (caretaker committees) na nufin jihohi suna ƙwace ikon ƙananan hukumomi, wanda ya saɓa wa kundin tsarin mulki na 1999.

Sai dai duk da shafe watanni 18 da yanke hukuncin, binciken majiyar mu ya nuna cewa har yanzu ba a aiwatar da shi yadda ya kamata ba.

Har yanzu ana ci gaba da tura kuɗaɗen ƙananan hukumomi ta hannun gwamnatocin jihohi, lamarin da ke haifar da jinkiri da saɓani tsakanin Babban Bankin Najeriya (CBN), gwamnatocin jihohi, ƙananan hukumomi da sauran hukumomi.

Bincike ya nuna cewa gwamnatocin jihohi sun ci gaba da sarrafa ƙalla Naira tiriliyan 7.43 da aka ware wa ƙananan hukumomi daga Yuli 2024 zuwa Disamba 2025, duk da hukuncin Kotun Ƙoli da ya umurci biyan kuɗin kai tsaye.

Binciken rabon kuɗaɗen FAAC ya nuna cewa an ware wa ƙananan hukumomi N7.43tn a cikin watanni 18, daga Yuli zuwa Disamba 2024 da kuma duk shekara ta 2025, duk da cewa tsarin biyan kuɗin kai tsaye bai canza sosai ba.

A rabin shekarar 2024 na biyu kadai, ƙananan hukumomi sun karɓi N2.08tn, yayin da adadin ya tashi zuwa N5.35tn a shekarar 2025.

Duk da ƙarin kuɗaɗen shiga, ana ci gaba da biyan su ne ta tsohon tsarin Asusun Haɗin Gwiwar Ƙananan Hukumomi da jihohi (State Joint Local Government Account), wanda ke bai wa gwamnonin jihohi cikakken tasiri kan kuɗaɗen ƙananan hukumomi.

A wata hira da aka yi da shi a Abuja, Babban Sakatare na ALGON, Muhammed Abubakar, ya tabbatar da goyon bayan ƙungiyar ga shirin Shugaba Tinubu na tilasta cire kuɗaɗen ƙananan hukumomi kai tsaye daga FAAC.

Muhammed ya ce Shugaban Ƙasa ya gargaɗi gwamnoni kai tsaye, kuma ya jingina hakan ne da hukuncin Kotun Ƙoli, wanda ya bayyana a matsayin hukumar shari’a mafi ƙololuwa a ƙasar nan.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Jirgin Sojojin Ruwa Yayi Gobara A Cross River
Next Post: Shugabannin Kasashen Sahel Sunyi Taro a Mali

Karin Labarai Masu Alaka

NLC Ta Yabawa Gwamnan Gombe Inuwa Yahaya Najeriya
Hukumar ‘Yan Sanda Ta Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe Afrika
Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet Labarai
Rikici Ya Barke A Kano Bayan Kashe Wani Matashi Da Ake Zargi Da Kashe Ladani Najeriya
Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba Kiwon Lafiya
Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kotu A Kasar Tunisiya Ta Daure Wani Babban Dan Kasuwa Da Wasu ‘Yan Majalisa Afrika
  • FIFA, Ta Tabbatar Da Ranar Mika Sunayen ‘Yan Wasa AFCON 2025. Wasanni
  • Shirin Dare 26.11.2025 Rediyo
  • Shugaba Tinubu Ya Yayi Magana Game Da Kafa ‘Yan Sandan Jihohi Najeriya
  • Gwamnatin Gombe Ta Dauki Sabbin Matakan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ankara Gano Wani Abu Mai Kama Da Abun Fashewa A Jabo Jihar Sokoto Tsaro
  • Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi Najeriya
  • Birtaniya Ta Bukaci Israela Ta Janye Shawarar Fadada Iko Da Kogin Jordan Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.