Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Fara Azumin Watan Ramadan A Najeriya Da Sassan Duniya 
Published: February 18, 2026 at 3:56 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

An Fara Azumin Watan Ramadana Na Bana a Najeriya Da Sassan Duniya

A Larabar nan 18 ga watan Febrairu 2026 a ka fara azumin watan Ramadana a Najeriya, Saudiyya da kasashen musulmi da dama.

Wannan ya biyo bayan ganin jinjirin watan Ramadana yayin da watan Sha’aban yayi kwana 29.

Wannan Shekarar Shehun Borno Alhaji Garbai Umar Elkenemi ke sanarda ganin watan a madadin mai alfarma Sarkin musulmi Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar wanda rahotanni su ka bayyana cewa ba ya kasa.

Wannan shi ne kusan karo na farko a tarihin shekarun nan da Shehun Borno ke ba da sanarwar kuma dama shi ne mataimakin shugaban majalisar sarakuna na Arewa.

Garbai Elkenemi ya bukaci musulmi su yi amfani da damar wajen yi wa shugabanni da kasa addu’ar alheri.

Malamai na kira ga masu hannu da shuni da ma ‘yan kasuwa su sa tallafi ko rangwame a farashin kayan masarufi.

Sheikh Abdullahi Bala Lau babban malami ne na sunnah a Najeriya wanda ya nuna muhimmancin rangwame a watan azumi.

Hakika musulmi kan yi amfani da watan na azumi wajen ninka kwazo a ibada da yin dogayen sallolin nafila.

Tuni majalisun tafsiri sun fara gabatarda zama inda bana Khalifan Shehu Dahiru Bauchi wato Sayyadi Ibrahim Dahiru Bauchi ya bude tafsirin Shehi wanda Allah ya yi wa rasuwa a kwanakin baya. Shehu kan gudanar da tafsirin a Kaduna a tsawon shekaru masu yawa.

Izala kadai ta tura fiye da malamai 2000 a ciki da wajen Najeriya don gabatarda tafsiri.

Ga Cikekken rahoton Nasiru Adamu El-Hikaya

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/02/RAMADAN-FAST-2026-HIJRA-1447-COMMENCES.mp3
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Rediyo, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Kamfanin Dangote Zai Sayo Na’urori Daga Kasar China
Next Post: Musulmai A Kasashen Duniya Da Dama Sunfara Azumin Ramadan

Karin Labarai Masu Alaka

Majalisar Dokokin Rivers Zata Tsige Fubara Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sojojin Amurka Sun Kutsa Cikin Kasar Iran Labarai
Gwamnan Jihar Adamawa Fintiri Ya Koma APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Hukumar NDLEA Ta Kama Wata Mata Da cikin Bogi Na ƙwaya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kungiyar MDD Ta Bukaci Ayi Bincike Game Da Kashe ‘Yan Iran Sauran Duniya
An Canza Shugabannin Hukumar Hakar Ma’adanai A Congo Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Iran Ta Bukaci Duniya Ta Shirya Domin Fuskantar Tsadan Mai Amurka
  • Zulum Ya Rushe Majalisar Zartarwa Ta Jihar Borno Afrika
  • Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia Afrika
  • Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
  • Rashin Kyawun Hanyoyi Babbar Matsalace A Najeriya Afrika
  • Farashin Mai Ya Cigaba Da Tashi Afrika
  • Yeriman Ingila Ya Mayarwa Trump Martani Amurka
  • Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.