Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Fara Azumin Watan Ramadan A Najeriya Da Sassan Duniya 
Published: February 18, 2026 at 3:56 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

An Fara Azumin Watan Ramadana Na Bana a Najeriya Da Sassan Duniya

A Larabar nan 18 ga watan Febrairu 2026 a ka fara azumin watan Ramadana a Najeriya, Saudiyya da kasashen musulmi da dama.

Wannan ya biyo bayan ganin jinjirin watan Ramadana yayin da watan Sha’aban yayi kwana 29.

Wannan Shekarar Shehun Borno Alhaji Garbai Umar Elkenemi ke sanarda ganin watan a madadin mai alfarma Sarkin musulmi Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar wanda rahotanni su ka bayyana cewa ba ya kasa.

Wannan shi ne kusan karo na farko a tarihin shekarun nan da Shehun Borno ke ba da sanarwar kuma dama shi ne mataimakin shugaban majalisar sarakuna na Arewa.

Garbai Elkenemi ya bukaci musulmi su yi amfani da damar wajen yi wa shugabanni da kasa addu’ar alheri.

Malamai na kira ga masu hannu da shuni da ma ‘yan kasuwa su sa tallafi ko rangwame a farashin kayan masarufi.

Sheikh Abdullahi Bala Lau babban malami ne na sunnah a Najeriya wanda ya nuna muhimmancin rangwame a watan azumi.

Hakika musulmi kan yi amfani da watan na azumi wajen ninka kwazo a ibada da yin dogayen sallolin nafila.

Tuni majalisun tafsiri sun fara gabatarda zama inda bana Khalifan Shehu Dahiru Bauchi wato Sayyadi Ibrahim Dahiru Bauchi ya bude tafsirin Shehi wanda Allah ya yi wa rasuwa a kwanakin baya. Shehu kan gudanar da tafsirin a Kaduna a tsawon shekaru masu yawa.

Izala kadai ta tura fiye da malamai 2000 a ciki da wajen Najeriya don gabatarda tafsiri.

Ga Cikekken rahoton Nasiru Adamu El-Hikaya

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/02/RAMADAN-FAST-2026-HIJRA-1447-COMMENCES.mp3
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Rediyo, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Kamfanin Dangote Zai Sayo Na’urori Daga Kasar China
Next Post: Musulmai A Kasashen Duniya Da Dama Sunfara Azumin Ramadan

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Trump Tana Cigaba Da Korar Baki Daga Amurka Afrika
Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
“Hotuna” An Sako Daliban Makarantar St. Mary’s Su 100 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Koriya Ta Arewa Ya Goyi Bayan Iran Wajen Zaben Sabon Jagora Mojtaba Khameni Afrika
Magajin Garin Istanbul Dake Kurkuku Ya Bukaci A Gudanar Da Zabe Labarai
China Ta Kori Wakilan Majalisar Dokoki Uku A Kasar Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC Labarai
  • Kasashe Biyar Zasu Tura Sojoji Domin Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya A Gaza Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Samar Da Dala Kusan Biliyan Biyu Don Yakar Polio Labarai
  • Shugaban Koriya Ta Arewa Ya Gabatar Da Gwajin Makami Mai Linzami Afrika
  • Lakurawa Sun Kashe A Ƙalla A Mutane 34 A Jihar Kebbi Labarai
  • Kamfanin Mai Mallakar Saudiya Aramco Zai Sanja Hanyar Fitar Da Danyen Mai Labarai
  • An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba. Afrika
  • An Tsinci Gawar Yarinya A Gombe Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.