Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

NYSC – Sai An Gabatar Da Takardar NERD Kafin Shiga Bautar Ƙasa
Published: May 19, 2026 at 10:42 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar ‘yan yiwa Ƙasa Hidima ta Najeriya, National Youth Service Corps, ta bayyana cewa daga yanzu za ta riƙa tura masu yi wa ƙasa hidima ne kawai idan sun gabatar da takardar shaidar tantancewa daga Nigeria Education Repository and Databank.

Babban Daraktan hukumar, Birgediya Janar Olakunle Nafiu, ne ya sanar da hakan yayin taron shirin tura masu yi wa ƙasa hidima na rukuni na “B” na shekarar 2026 da aka gudanar a Abuja.

Ya ce matakin wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnatin Najeriya na daƙile amfani da jabun takardun kammala karatu tare da tabbatar da cewa sahihan waɗanda suka kammala karatu ne kawai ake bai wa damar gudanar da bautar ƙasa.

Janar Nafiu ya yi kira ga jami’o’i da sauran cibiyoyin ilimi masu fitar da ɗalibai zuwa bautar ƙasa da su ƙara wayar da kan ɗalibansu kan muhimmancin bin sabon tsarin tare da tabbatar da cikakken aiwatar da shi.

A cewarsa, aikin tantancewa da tura masu yi wa ƙasa hidima ba nauyin NYSC kaɗai ba ne, yana mai jaddada muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin hukumomin gwamnati, cibiyoyin ilimi, jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da gaskiya, inganci da amincin tsarin bautar ƙasa.

Tun da farko, Daraktar Sashen Tura Masu Yi wa Ƙasa Hidima ta NYSC, Misis Rachel Ideawor, ta bayyana taron a matsayin wata muhimmiyar dama ta ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumar da cibiyoyin ilimi domin inganta tsarin tura masu yi wa ƙasa hidima a faɗin ƙasar.

Ta kuma buƙaci jami’an kula da harkokin ɗalibai su gudanar da aikinsu cikin gaskiya da riƙon amana tare da tabbatar da cewa bayanan da ake aikawa sun dace da ainihin bayanan masu shirin bautar ƙasa.

Taron ya samu halartar wakilai daga Joint Admissions and Matriculation Board, National Universities Commission, National Board for Technical Education, Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da sauran hukumomin da ke da ruwa da tsaki a harkar ilimi da bautar ƙasa a Najeriya.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Shirye-Shirye

Post navigation

Previous Post: Sanata Goje: Sakamakon Zaben Daga Abuja Zai Fito
Next Post: Zargin Tauye Ka’idojin Zabe: Malam Pantami Ya Janye Daga Takara

Karin Labarai Masu Alaka

Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya Labarai
Kasar Saudiya Zata Cika Azumi Talatin Kimiya
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tinubu Na Kokarin Rage Tsadar Sufuri Ta Hanyar Shirin CNG Afrika
Sarkin Gombe Ya Ziyarci Gwamna Inuwa Yahaya Afrika
Burkina Faso: Mun Kama Sojojin Najeriya da Jirgin Yaki Bisa Shigowa Ba Bisa Ka’ida Ba Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shirin Dare 26.11.2025 Rediyo
  • Farashin Danyen Mai Da Iskar Gas Ya Tashi Afrika
  • An Bude Gasar Kwallon Kafa Ta Mata A Najeriya NWFL 2025 Wasanni
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Gabatar Da Kudi Fiye Da Naira Triliyan 58 A Matsayin Kasafin 2026 Najeriya
  • Fiye Da Mutane Miliyan Hudu Suna Fuskantar Barazanar Yunwa A Somaliya Sauran Duniya
  • Amurka Zata Fara Sayar Da Maganin Hana Kiba Da Jin Yunwa Amurka
  • FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca Wasanni
  • Najeriya Da Amurka Sun Karfafa Alakar Tsaro Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.