Hukumar ‘yan yiwa Ƙasa Hidima ta Najeriya, National Youth Service Corps, ta bayyana cewa daga yanzu za ta riƙa tura masu yi wa ƙasa hidima ne kawai idan sun gabatar da takardar shaidar tantancewa daga Nigeria Education Repository and Databank.
Babban Daraktan hukumar, Birgediya Janar Olakunle Nafiu, ne ya sanar da hakan yayin taron shirin tura masu yi wa ƙasa hidima na rukuni na “B” na shekarar 2026 da aka gudanar a Abuja.
Ya ce matakin wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnatin Najeriya na daƙile amfani da jabun takardun kammala karatu tare da tabbatar da cewa sahihan waɗanda suka kammala karatu ne kawai ake bai wa damar gudanar da bautar ƙasa.
Janar Nafiu ya yi kira ga jami’o’i da sauran cibiyoyin ilimi masu fitar da ɗalibai zuwa bautar ƙasa da su ƙara wayar da kan ɗalibansu kan muhimmancin bin sabon tsarin tare da tabbatar da cikakken aiwatar da shi.
A cewarsa, aikin tantancewa da tura masu yi wa ƙasa hidima ba nauyin NYSC kaɗai ba ne, yana mai jaddada muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin hukumomin gwamnati, cibiyoyin ilimi, jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki domin tabbatar da gaskiya, inganci da amincin tsarin bautar ƙasa.
Tun da farko, Daraktar Sashen Tura Masu Yi wa Ƙasa Hidima ta NYSC, Misis Rachel Ideawor, ta bayyana taron a matsayin wata muhimmiyar dama ta ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumar da cibiyoyin ilimi domin inganta tsarin tura masu yi wa ƙasa hidima a faɗin ƙasar.
Ta kuma buƙaci jami’an kula da harkokin ɗalibai su gudanar da aikinsu cikin gaskiya da riƙon amana tare da tabbatar da cewa bayanan da ake aikawa sun dace da ainihin bayanan masu shirin bautar ƙasa.
Taron ya samu halartar wakilai daga Joint Admissions and Matriculation Board, National Universities Commission, National Board for Technical Education, Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya da sauran hukumomin da ke da ruwa da tsaki a harkar ilimi da bautar ƙasa a Najeriya.


