Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya karɓi ziyarar gaisuwar Sallah daga Sarkin Gombe, Alhaji Dr. Abubakar Shehu Abubakar III, a Fadar Gwamnati, yayin bikin Eid-el-Fitr na bana.
Wannan ziyara, wadda ta zama al’ada a jihar, na bawa Sarkin damar taya Gwamna da al’ummar Gombe murnar kammala azumin watan Ramadan, tare da ƙarfafa dangantaka tsakanin hukumomin gargajiya da gwamnati.

Ga Rahoton Wakilin Amurka Ke Magana a Gombe Aliyu Bala Gerengi


