Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko
Published: December 12, 2025 at 9:43 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 13, 2025

Nan bada jimawa ba Makarantun Allo zasu yi gogayya da takwarorinsu na Boko dake faɗin Kasa. ”in ji Minitan Ilimi na Tarayyar Najeriya.

Ministan Ilimin Najeriya Dakta Tunji Alausa yace tsarin ingatawa tare da koyar da Karatun Allo da ilimin Tsangayu dake da manufar inganta karatu da rayuwar Almajirai da aka kaddamar ranar Litinin din data gabata, manufar samar da tsarin bai daya da za a rinka amfani da shi a matakin kasa baki daya.

 

 

 

 

 

 

Da yake karin haske dangane da wannan gagarumin sauyi da ma’aikatar ilimin ke kokarin aiwatarwa, maitaimakawa Ministan ilimin Najeriya kan ilimin Almajirai da Tsangayu hadi da makarantun Allo, Dr. Balarabe Shehu Kakale, Barden Tsangayu da Makarantun Allo na Kasar Hausa yace nan bada jimawa ba Makarantun Allo zasu yi gogayya da takwaroinsu na Boko dake faɗin kasar.

Haka zalika, Dr. Kakale, ya kara da cewa kafin akai ga wannan matsayar, sai da suka karade daukacin shiyyoyin siyasa shida na Najeriya inda suka tattauna da masu ruwa da tsaki da suka hada da Malamai da sarakuna da Kungiyar kiristoci ta Najeriya wato CAN, sai dai ya bayyana bukatar dake akwai wajen ganin gwamnatocin jihohi sun kara damba domin kaiwa ga cikakkiyar Nasara.

Tun da fari, Dr. Balarabe Shehu Kakale tsohon danmajalisar tarayya Najeriya, ya yabawa Ministan ilimin Najeriya Dakta Tunji Alausa da Ministan kasa a ma’aikatar ilimin kasar Dr. Suwaiba Ahmed da kuma shugaban hukumar kula da ilimin Almajirai da yara da basa zuwa makaranta ta kasar Dr. Mohammed Sani Idris hadi da jagororin addinai da sarakuna bisa matakan da suke dauka na inganta ilimin Almajirai dama rayuwar yaran da basa zuwa makaranta ta hanyar koyar da su sa’o’in hannu da zai basu damar dogaro da kan su.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Amurka Na Gargadin Rwanda Da Ta Mutunta Alkawali
Next Post: Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta

Karin Labarai Masu Alaka

Bankin Duniya Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Afirka Da Yankin Sahara Afrika
Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA. Labarai
Gwamnatin Tarayyar Najeriya Zata Raba Taki Ga Manoma Afrika
Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno Afrika
Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar Afrika
Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kungiyar EU Zata Taimakawa Somalia Da Kudade Labarai
  • Kasashen Turai: Bazamu Yarda Da Dokar Harajin Trump Ba Labarai
  • Karamar Sallah: Hukumar Kashe Gobara A Gombe Ta Kuduri Aniyar Kare Al’umma Afrika
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
  • An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
  • Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA. Labarai
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Kara Sace Mutane A Jihar Naija! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.