Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko
Published: December 12, 2025 at 9:43 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 13, 2025

Nan bada jimawa ba Makarantun Allo zasu yi gogayya da takwarorinsu na Boko dake faɗin Kasa. ”in ji Minitan Ilimi na Tarayyar Najeriya.

Ministan Ilimin Najeriya Dakta Tunji Alausa yace tsarin ingatawa tare da koyar da Karatun Allo da ilimin Tsangayu dake da manufar inganta karatu da rayuwar Almajirai da aka kaddamar ranar Litinin din data gabata, manufar samar da tsarin bai daya da za a rinka amfani da shi a matakin kasa baki daya.

 

 

 

 

 

 

Da yake karin haske dangane da wannan gagarumin sauyi da ma’aikatar ilimin ke kokarin aiwatarwa, maitaimakawa Ministan ilimin Najeriya kan ilimin Almajirai da Tsangayu hadi da makarantun Allo, Dr. Balarabe Shehu Kakale, Barden Tsangayu da Makarantun Allo na Kasar Hausa yace nan bada jimawa ba Makarantun Allo zasu yi gogayya da takwaroinsu na Boko dake faɗin kasar.

Haka zalika, Dr. Kakale, ya kara da cewa kafin akai ga wannan matsayar, sai da suka karade daukacin shiyyoyin siyasa shida na Najeriya inda suka tattauna da masu ruwa da tsaki da suka hada da Malamai da sarakuna da Kungiyar kiristoci ta Najeriya wato CAN, sai dai ya bayyana bukatar dake akwai wajen ganin gwamnatocin jihohi sun kara damba domin kaiwa ga cikakkiyar Nasara.

Tun da fari, Dr. Balarabe Shehu Kakale tsohon danmajalisar tarayya Najeriya, ya yabawa Ministan ilimin Najeriya Dakta Tunji Alausa da Ministan kasa a ma’aikatar ilimin kasar Dr. Suwaiba Ahmed da kuma shugaban hukumar kula da ilimin Almajirai da yara da basa zuwa makaranta ta kasar Dr. Mohammed Sani Idris hadi da jagororin addinai da sarakuna bisa matakan da suke dauka na inganta ilimin Almajirai dama rayuwar yaran da basa zuwa makaranta ta hanyar koyar da su sa’o’in hannu da zai basu damar dogaro da kan su.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Amurka Na Gargadin Rwanda Da Ta Mutunta Alkawali
Next Post: Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta

Karin Labarai Masu Alaka

Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yakin Gabas Ta Tsakiya Afrika
Mabiya Addinin Kirista Da ‘Yan Bindiga Suka Sace Sun Kubuta Labarai
China Ta Kori Wakilan Majalisar Dokoki Uku A Kasar Labarai
‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutun Sallar Azumi Afrika
Shugaban Kasar Ukraine Yace Rasha Tana Bawa Iran Bayanan Sirri Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu Najeriya
  • Turkiyya Tana Gudanar Da Binciken Kasar Da Suka Kona Tutar Ta Tsaro
  • Masu Goyon Bayan Palasdinawa Sunyi Gangamin Zanga Zanga A Australia Labarai
  • FIFA Ta Yi Wa Malaysia Kaca-kaca Wasanni
  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina Najeriya
  • An Fara Azumin Watan Ramadan A Najeriya Da Sassan Duniya  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kamfanin Dangote Zai Sayo Na’urori Daga Kasar China Kimiya
  • Rivers: ‘Yan Majalisa 16 Sun Canza Sheka Zuwa APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.