Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026
Published: December 7, 2025 at 4:50 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Bauchi ta bayyana cewar tana duba yuwuwar bude makarantu a farkon sabon shekara mai zuwa bayan hutun karshen shekara, yayin da take ci gaba da tantance yanayin tsaro a fadin jihar.

Majiyar mu ta habarto cewa, Kwamishinan Ilimi na Jihar Bauchi, Dr. Muhammad Lawal Rimin Zayam, ya ce akwai yuwuwar makarantu su koma karatu a farkon shekarar 2026 tare da shirya jarabawar zangon farko nan take bayan komawa.

A ranar 23 ga watan Nuwamba, na shekarar 2025 ne Ma’aikatar Ilimi ta bayar da umarnin rufe dukkannin makarantun jihar, har da manyan makarantu, sakamakon yawaitar sace sacen dalibai da ake fama da su a sassan kasa.

A cewar Kwamishinan, lokacin da aka rufe makarantun, saura kimanin makonni biyu ne a kammala zangon karatu da ake ciki.

Ya ce gwamnati za ta yi amfani da wannan damar wajen gudanar da gyar gyare a makaranti jihar domin samar da yanayi mai kyau da aminci ga dalibai lokacin da suka koma Makarantu domin kyautata ilimi.

Kwamishinan ya bayyana cewa shirin da ake yi na komawa makarantu ya yi daidai da shirinSafe Schools Initiative, inda ya kara da cewa yawancin makarantun jihar yanzu suna da katanga domin karfafa tsaro.

Ya kuma shawarci dalibai su ci gaba da karatu a lokacin hutun ta hanyar amfani da Fasahar zamani ta Nigeria e-learning platform, wato tsarin koyo da aka yi amfani da shi a lokacin kulle na COVID-19.

Kwamishinan ya kara da cewa dalibai za su ci gaba da zangon karatu ba tare da wani hutun karshen zangon ba, domin cike gibin lokacin da aka rasa yayin rufe makarantun.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade
Next Post: Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Na Yi Murabus Ne Don Amurka Ta Keta Haddin Iraniyawa Amurka
Hamas Ta Kwance Damara Afrika
NYSC – Sai An Gabatar Da Takardar NERD Kafin Shiga Bautar Ƙasa Afrika
Rundunar ‘Yan Sandan Kebbi Ta Dakile Yunkurin Garkuwa Da Mutune, Ta Kama Masu Laifi Afrika
Gwamna Inuwa Yahaya Ya Amince Da Gyaran Fadar Sarkin Gombe Afrika
Jami’ar ABU Zaria Ta Karbi Kudade Naira Bilyan 1.3 Daga Shirin Nelfund Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Bola Tinubu Ta Raba Taraktoci Dubu Biyu Domin Inganta Noma Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasashen Daular Larabawa Tare Da Saudiya Da Jordan Sunyi Allah Wadai Da kasar Israel Afrika
  • An Bukaci Sabbin Shugabanni Su Yi Jagoranci Nagari da Inganta Ayyukan Jama’a Labarai
  • Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware Labarai
  • CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar China Tana Cigaba Da Nuna Fin Karfi Ga Kasar Taiwan Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.