Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026
Published: December 7, 2025 at 4:50 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Bauchi ta bayyana cewar tana duba yuwuwar bude makarantu a farkon sabon shekara mai zuwa bayan hutun karshen shekara, yayin da take ci gaba da tantance yanayin tsaro a fadin jihar.

Majiyar mu ta habarto cewa, Kwamishinan Ilimi na Jihar Bauchi, Dr. Muhammad Lawal Rimin Zayam, ya ce akwai yuwuwar makarantu su koma karatu a farkon shekarar 2026 tare da shirya jarabawar zangon farko nan take bayan komawa.

A ranar 23 ga watan Nuwamba, na shekarar 2025 ne Ma’aikatar Ilimi ta bayar da umarnin rufe dukkannin makarantun jihar, har da manyan makarantu, sakamakon yawaitar sace sacen dalibai da ake fama da su a sassan kasa.

A cewar Kwamishinan, lokacin da aka rufe makarantun, saura kimanin makonni biyu ne a kammala zangon karatu da ake ciki.

Ya ce gwamnati za ta yi amfani da wannan damar wajen gudanar da gyar gyare a makaranti jihar domin samar da yanayi mai kyau da aminci ga dalibai lokacin da suka koma Makarantu domin kyautata ilimi.

Kwamishinan ya bayyana cewa shirin da ake yi na komawa makarantu ya yi daidai da shirinSafe Schools Initiative, inda ya kara da cewa yawancin makarantun jihar yanzu suna da katanga domin karfafa tsaro.

Ya kuma shawarci dalibai su ci gaba da karatu a lokacin hutun ta hanyar amfani da Fasahar zamani ta Nigeria e-learning platform, wato tsarin koyo da aka yi amfani da shi a lokacin kulle na COVID-19.

Kwamishinan ya kara da cewa dalibai za su ci gaba da zangon karatu ba tare da wani hutun karshen zangon ba, domin cike gibin lokacin da aka rasa yayin rufe makarantun.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade
Next Post: Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Tawagar Masu Yi Wa Maniyyata Hidima Za Ta Tashi Zuwa Saudiyya Afrika
Birtaniya Zata Fara Raba Rigakafin Allurar Cutar Sankara Kimiya
Sojojin Kasar Isra’ila Sun Kashe Wani Babban Kwamandan Hamas Labarai
‘Yan Majalisar Wakilai 17 Sun Fice Daga ADC Afrika
Hukumar MDD Tace Wadanda Suka Mutu A Harin Sudan Sun Haura 70 Afrika
Dakarun Sakai A Kasar Sudan Sun Kashe Mutane 28 A Wani Farmaki Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Israela Zata Gina Sansani A Gaza Afrika
  • Rasha Na Cigaba Da Kai Hare-Haren Makamai Masu Linzami Ga Ukrain Labarai
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Trump Yace Amurka Zata Janye Yaki Da Iran Afrika
  • Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya Amurka
  • A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela Amurka
  • An Gudanar Da Zanga-Zanga A Guinea-Bissau Afrika
  • An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.