Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026
Published: December 7, 2025 at 4:50 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Bauchi ta bayyana cewar tana duba yuwuwar bude makarantu a farkon sabon shekara mai zuwa bayan hutun karshen shekara, yayin da take ci gaba da tantance yanayin tsaro a fadin jihar.

Majiyar mu ta habarto cewa, Kwamishinan Ilimi na Jihar Bauchi, Dr. Muhammad Lawal Rimin Zayam, ya ce akwai yuwuwar makarantu su koma karatu a farkon shekarar 2026 tare da shirya jarabawar zangon farko nan take bayan komawa.

A ranar 23 ga watan Nuwamba, na shekarar 2025 ne Ma’aikatar Ilimi ta bayar da umarnin rufe dukkannin makarantun jihar, har da manyan makarantu, sakamakon yawaitar sace sacen dalibai da ake fama da su a sassan kasa.

A cewar Kwamishinan, lokacin da aka rufe makarantun, saura kimanin makonni biyu ne a kammala zangon karatu da ake ciki.

Ya ce gwamnati za ta yi amfani da wannan damar wajen gudanar da gyar gyare a makaranti jihar domin samar da yanayi mai kyau da aminci ga dalibai lokacin da suka koma Makarantu domin kyautata ilimi.

Kwamishinan ya bayyana cewa shirin da ake yi na komawa makarantu ya yi daidai da shirinSafe Schools Initiative, inda ya kara da cewa yawancin makarantun jihar yanzu suna da katanga domin karfafa tsaro.

Ya kuma shawarci dalibai su ci gaba da karatu a lokacin hutun ta hanyar amfani da Fasahar zamani ta Nigeria e-learning platform, wato tsarin koyo da aka yi amfani da shi a lokacin kulle na COVID-19.

Kwamishinan ya kara da cewa dalibai za su ci gaba da zangon karatu ba tare da wani hutun karshen zangon ba, domin cike gibin lokacin da aka rasa yayin rufe makarantun.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade
Next Post: Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Tattalin Arzikin Kasar Bahrain Ya Bunkasa Sakamakon Ruruwar Masu Yawon Bude Ido Labarai
‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya Labarai
Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia Afrika
Hukumomin Tsaron Najeriya Ne Suka Bukaci Amurka Ta Turo Musu Sojoji Amurka
Shugaba Yoweri Musevini Ya Zamo Shugaban Uganda Na 7 Yana Da Shekaru 81 Kuma Ya Shafe Shekaru 50 A Mulki Labarai
Wani Dan Bindiga Ya Harbi Dakarun Tsaron Cikin Gida Su Biyu A Washington DC Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe
  • Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta
  • Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Hukumar Zabe A Najeriya Ta Cigaba Da Rijistar Katin Zabe Labarai
  • Azumin Ramadan Yahadu Da Azumin Lent Da Mabiya Addinin Kirista Sukeyi A Wannan Shekarar Labarai
  • Na Duke Tsohon Ciniki Shirye-Shirye
  • Suvr Jahun: Ya Kamata Obasanjo Ya Bar Al’umar Ƙasa Su Fito Da Wadda Suke So 2027 Najeriya
  • Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf Ya Gana Da Shugaba Tinubu Siyasa
  • Iran Ta Rufe Sararin Samaniyar Ta Labarai
  • Jakadan Amurka A Poland Ya Yanke Hulda Da Kakakin Majalisar Kasar Labarai
  • Amurka Ta Gabatarwa Sassan Dake Yakar Juna A Sudan da Shirin Tsagaita Wuta Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.