Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba
Published: December 7, 2025 at 5:16 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Tun fiye da shekaru sittin da mafi yawan kasashen Afirka suka sami ‘yancin kai, masana sun bayyana cewa har yanzu nahiyar na fama da tsarin mulkin mallaka da rashin samun ‘yanci a fannoni daban-daban na rayuwa.
A wani taro da masana daga kasashen duniya suka halarta, da masu fafutukar ‘yanci da hukumomi da dalibai daga kasashe daban-daban na Afirka, wadanda suka taru a Jami’ar Jos, an gabatar da kasidu da suka yi nazari kan makomar Nahiyar Afirka da hanyoyin samar da mafita.
Taron na tunawa da wani matubuci da fafutuka, Frantz Fanon da yayi rubuce-rubuce da suka zame kamar wahayi kan makomar nahiyar Afirka a fannonin damokradiyya, gazawar shugabanci da sauransu.
Malam Jibrin Ibrahim na cibiyar damokradiyya da ci gaba dake Abuja, Najeriya, yace taron yayi nazari ne kan rashin tasiri da ‘yancin kai a Afirka ya kasance.
Shima Malam Yunusa Zakari-Ya’u na cibiyar fasahar sadarwa da ci gaba dake Kano, Najeriya, yace yawan juyin mulki da ake samu a wassu kasahen Afirka, saboda rashin adalcin shugabanni ne.
Komared Sam Magaji, malami a Jami’ar Jos, yace suna horadda dalibai su san yadda shugabanni a baya suka yi mulki, da yadda daliban zasu yi nazarin abubuwan dake faruwa yanzu, da yadda za’a yi gyara nan gaba.
Mr Charles Toheyo, malami a Jami’ar Nkerere dake kasar Uganda, yace idan har shugabannan dake mulki basu sauya tunaninsu ta yadda zasu kyautata wa al’umma ba, to ba shakka za’a ci gaba da zaman tankiya.
Adam Khalid, dalibi a Jami’ar Jos, yace matasa a Afirka a shirye suke su kawo sauyi, sai dai har yanzu basu sami jagoranci daga dattawa ba, saboda dattawan kansu kadai suka sani.
A taron na wuni biyu, an gabatar da kasidu kimanin saba’in, da suka kunshi samarda mafita kan matsalolin da suka hana kasashen Afirka samun walwala da ci gaba.
https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/DAMOKRADIYYA-A-AFIRKA.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026
Next Post: Marc Brys: “Eto’o Baiyi Adalci Ga Onana, Da Vincent, Ba”

Karin Labarai Masu Alaka

Rikicin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Man Fetur A Najeriya Afrika
’Yar Kasuwa Ta Tsallake Rijiya Da Baya Bayan Hari Da Saurayinta Ya Kai Mata Afrika
Akwai Bukatar APC Tayi Gyare-Gyare Kafun Zabe Afrika
Mataimakin Shugaban Kasa Ya Sauka A Jihar Kwara Labarai
Jihar Gombe Tayi Fice A Bangaren Inganta Lafiya Matakin Farko Najeriya
Shugaba Tinubu Ya Ware Kudade Domin Bunkasa Rayuwar ‘Yan Najeriya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kanal Sani: Idan ‘Yan-Ta’adda Zasu Mutunta Sulhu To Gwamnati Ta Duba Hakan Labarai
  • Za’a Dauko Messi Aro Zuwa Barcelona Deco Wasanni
  • Jami’an Tsaro Suna Farautar Wasu ‘Yan Ta’adda A Najeriya Afrika
  • An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali Tsaro
  • Shugaban Kasar Uganda Yana Kokarin Mayar Da Mulkin Kasar Na Gado Labarai
  • Abu Mafi Daukar Hankali A Wasan Dambe Na Yau Wasanni
  • Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.