Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika

Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba
Published: December 7, 2025 at 5:16 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Tun fiye da shekaru sittin da mafi yawan kasashen Afirka suka sami ‘yancin kai, masana sun bayyana cewa har yanzu nahiyar na fama da tsarin mulkin mallaka da rashin samun ‘yanci a fannoni daban-daban na rayuwa.
A wani taro da masana daga kasashen duniya suka halarta, da masu fafutukar ‘yanci da hukumomi da dalibai daga kasashe daban-daban na Afirka, wadanda suka taru a Jami’ar Jos, an gabatar da kasidu da suka yi nazari kan makomar Nahiyar Afirka da hanyoyin samar da mafita.
Taron na tunawa da wani matubuci da fafutuka, Frantz Fanon da yayi rubuce-rubuce da suka zame kamar wahayi kan makomar nahiyar Afirka a fannonin damokradiyya, gazawar shugabanci da sauransu.
Malam Jibrin Ibrahim na cibiyar damokradiyya da ci gaba dake Abuja, Najeriya, yace taron yayi nazari ne kan rashin tasiri da ‘yancin kai a Afirka ya kasance.
Shima Malam Yunusa Zakari-Ya’u na cibiyar fasahar sadarwa da ci gaba dake Kano, Najeriya, yace yawan juyin mulki da ake samu a wassu kasahen Afirka, saboda rashin adalcin shugabanni ne.
Komared Sam Magaji, malami a Jami’ar Jos, yace suna horadda dalibai su san yadda shugabanni a baya suka yi mulki, da yadda daliban zasu yi nazarin abubuwan dake faruwa yanzu, da yadda za’a yi gyara nan gaba.
Mr Charles Toheyo, malami a Jami’ar Nkerere dake kasar Uganda, yace idan har shugabannan dake mulki basu sauya tunaninsu ta yadda zasu kyautata wa al’umma ba, to ba shakka za’a ci gaba da zaman tankiya.
Adam Khalid, dalibi a Jami’ar Jos, yace matasa a Afirka a shirye suke su kawo sauyi, sai dai har yanzu basu sami jagoranci daga dattawa ba, saboda dattawan kansu kadai suka sani.
A taron na wuni biyu, an gabatar da kasidu kimanin saba’in, da suka kunshi samarda mafita kan matsalolin da suka hana kasashen Afirka samun walwala da ci gaba.
https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/DAMOKRADIYYA-A-AFIRKA.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026
Next Post: Marc Brys: “Eto’o Baiyi Adalci Ga Onana, Da Vincent, Ba”

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutu Najeriya
Gwamnatin Sokoto Tabada Umarnin Biyan Albashin Watan Fabrairu Labarai
Amurka Zata Hana Kwankwaso Shiga Kasar Amurka
Akwai Alamar Shawarwari Tsakanin Amurka Da Turai Zai Kawo Karshen Yakin Rasha Amurka
Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
Rundunar Sojin Najeriya Ta Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Jihar Borno Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Birtaniya Zata Hana Jiragen Ruwan Rasha Wucewa Afrika
  • Chelle: Rashin Jituwa Tsakanin Osimhen Da Lookman Matsala Ce Ta Cikin Gida Wasanni
  • An Gudanar Da Idin Karamar Sallah A Birnin Niamey Labarai
  • Gwamnatin Bauchi: Ta Kaddamar Da Kwamitin Ma’adanai Labarai
  • Isra’ila Tace Bazata Sake Kai Hari Kan Cibiyar Gas Ta Iran Ba Afrika
  • Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mataimakin Gwamnan Bayelsa Najeriya
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tsarin Haraji Mai Cike Da Ayoyin Tambaya Na Shirin Fara Aiki Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.