Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Amurka Na Gargadin Rwanda Da Ta Mutunta Alkawali
Published: December 12, 2025 at 8:48 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 13, 2025

Amurka ta zargi kasar Rwanda da laifin haddasa tashe-tashen hankula da kuma yaki a bayan da ‘yan tawayen kungiyar M23 da take goyon baya a gabashin kasar Kwango ta Kinshasa suka ci gaba da kai hare-hare da kwace yankuna.

Wannan farmaki na ‘yan tawayen na barazanar gurgunta kokarin shugaba Donald Trump na Amurka na kawo zaman lafiya a yankin.

Jakadan Amurka a Majalisar Dinkin Duniya, mike Waltz, ya fadawa Kwamitin Sulhu cewa zasu yi amfani da dukkan karfi da tasirin da suke da shi wajen tabbatar da cewa an hukumta masu gurgunta wanzuwar zaman lafiya.

Hare-haren ‘yan tawayen na baya-bayan nan sun kusanta da wannan fada zuwa bakin iyakar kasar da Burundi, wadda ta yi shekara da shekaru da girka sojojinta a gabashin Kwango bisa gayyatar gwamnatin kasar.

Wannan na kara fargabar cewa wannan rikici da ya janyo mutuwar dubban mutane zai kara yaduwa zuwa wasu sassan yankin.

Waltz ya fada a gaban Kwamitin Sulhun majalisar cewa Amurka tana kira ga Rwanda da ta mutunta alkawarin da ta dauka a karkashin yarjejeniyar da aka cimma, ta kuma mutunta ikon da gwamnatin Kwango take da shi na kare kasarta, da kuma ikonta na gayyatar sojojin kasar Burundi zuwa cikin Kwango domin su taimaka mata wajen kare kasar. 

 

Afrika

Post navigation

Previous Post: Akalla Mutane 8 Sun Mutu Biyo Bayan Bindiga Da Wata Tanka Tayi
Next Post: Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko

Karin Labarai Masu Alaka

Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta Duniya Zata Binciki Kasar Iran Afrika
Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin Afrika
Ministan Sadarwan Kasar Uganda Yayi Allah Wadai Da Kaiwa Bobi Wine Hari Afrika
Jami’in Diflomasiyyar Da Ake Zargi Da Kisan Prime minister Ya Daukaka Kara Afrika
Kasar Faransa Ta Karyata Cire Afirka Ta Kudu Daga G7 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Abun Da Kuke Buƙatar Sani Game Da Gasar Cin Kofin Ƙasashen Afirka 2025 Wasanni
  • Anfara Samun Sakamakon Wucin Gadi a Kasar Guinea Conakry Labarai
  • Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal Ya Bar PDP Ya Koma APC Labarai
  • Netanyahu Yana Neman Shawarwari Daga Hukumomin Lebanon Labarai
  • 2025 Ta Bar Baya Da Abubuwa Masu Ban Al’ajabi, 2026 Barka Da Zuwa! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi Labarai
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Jihar Filato Ya Karbi Katin APC Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.