Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jana’izar Jagoran Ƙolin Iran Ta Kawo Tsauraran Matakan Tsaro A Tehran Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika

Amurka Na Gargadin Rwanda Da Ta Mutunta Alkawali
Published: December 12, 2025 at 8:48 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 13, 2025

Amurka ta zargi kasar Rwanda da laifin haddasa tashe-tashen hankula da kuma yaki a bayan da ‘yan tawayen kungiyar M23 da take goyon baya a gabashin kasar Kwango ta Kinshasa suka ci gaba da kai hare-hare da kwace yankuna.

Wannan farmaki na ‘yan tawayen na barazanar gurgunta kokarin shugaba Donald Trump na Amurka na kawo zaman lafiya a yankin.

Jakadan Amurka a Majalisar Dinkin Duniya, mike Waltz, ya fadawa Kwamitin Sulhu cewa zasu yi amfani da dukkan karfi da tasirin da suke da shi wajen tabbatar da cewa an hukumta masu gurgunta wanzuwar zaman lafiya.

Hare-haren ‘yan tawayen na baya-bayan nan sun kusanta da wannan fada zuwa bakin iyakar kasar da Burundi, wadda ta yi shekara da shekaru da girka sojojinta a gabashin Kwango bisa gayyatar gwamnatin kasar.

Wannan na kara fargabar cewa wannan rikici da ya janyo mutuwar dubban mutane zai kara yaduwa zuwa wasu sassan yankin.

Waltz ya fada a gaban Kwamitin Sulhun majalisar cewa Amurka tana kira ga Rwanda da ta mutunta alkawarin da ta dauka a karkashin yarjejeniyar da aka cimma, ta kuma mutunta ikon da gwamnatin Kwango take da shi na kare kasarta, da kuma ikonta na gayyatar sojojin kasar Burundi zuwa cikin Kwango domin su taimaka mata wajen kare kasar. 

 

Afrika

Post navigation

Previous Post: Akalla Mutane 8 Sun Mutu Biyo Bayan Bindiga Da Wata Tanka Tayi
Next Post: Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko

Karin Labarai Masu Alaka

Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
Shugaban Hukumar Kwallon Kafa Ta Senegal Yaki Amincewa Da Hukuncin CFA Afrika
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Katsina Afrika
Rundunar Sojin KTK Ta Harba Makami Teku Afrika
Shugaban Kasar Afirka Ta Tsakiya Ya Roki Rasha Ta Taimakawa Kasar Afrika
Bankin Duniya Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Afirka Da Yankin Sahara Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jana’izar Jagoran Ƙolin Iran Ta Kawo Tsauraran Matakan Tsaro A Tehran
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasar Botswana Na Samun Kudaden Shiga Da Lu’ulu’u Labarai
  • Gabannin Harin Amurka Da Isra’ila Iran Farisa Ta Shirya Nata Afrika
  • Kudaden Shigan Kasar Namibia Ya Bunkasa Saboda Tashin Farashin Gwal Labarai
  • Shugaban Rasha Yafara Ganawa Da Jakadun Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Ukraine Amurka
  • Kungiyar Cigaban Al’ummar Tangale Tace Bata Goyon Bayan Kai Ziyara Wa Gwamnan Gombe Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Masu Zuba Jari A Birnin Paris Afrika
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Samun Sakamako Mai Kyau A Tattaunawa Da Amurka Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.