Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993
Published: October 19, 2025 at 3:12 AM | By: Newsdesk | Updated: November 16, 2025

Tsohon shugaban mulkin soja na Najeriya Janar Ibrahim Badamasi Babangida ya ce hakika marigayi Moshood Abiola ya lashe zaben watan Yuni na 1993 wanda gwamnatin sa ta soke.

Janar Babangida na magana ne a Abuja wajen taron kaddamar da littafin tarihin rayuwar sa ta aiki mai taken “A journey in service” da asusun gina dakin karatu na IBB a Minna.

“Na dau alhakin duk abun da gwamnati na ta gudanar, soke zaben 1993 na daga abubuwan da su ka zama masu tsauri a rayuwa ta” Inji Janar Babangida bayan tabbatar da cewa Abiola ya cika dukkan sharuddan lashe zaben wajen yawan kuri’a da kuma samun adadin yankuna.

Janar Babangida ya yabawa gwamnatin tsohon shugaba Buhari don aiyana Abiola a matsayin tsohon shugaban kasa duk da hakan ya faru bayan rayuwar sa.

Tsohon mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo da ya yi btar littafin mai shafi 420 a gaban mahalarta da su ka hada da shugaba Bola Tinubu da Janar Yakubu Gowon ya kawo bayanan yanda Babangida ya kwance damarar Dimka bayan kisan gilla ga Janar Murtala da kuma yanda juyin mulki ya kawo Buhari kan mulki a 1983 har sake juyin mulki a 1985 da Babangida ya hau da labarin su Janar Mamman Vatsa wanda a ka yankewa hukuncin kisa sanadiyyar shirin juyin mulki. Hakanan ya kawo lakabin Babangida da ya hada da MARADONA don yanda ba a gane matakin da zai dauka sai ya cimma nasara sai EVIL GENIUS da ke nuna hatsabibancin sa a aikin soja.

Janar Muhammad Barau mai ritaya ya ce ya yi aiki da Janar Babangida kuma har yau bai ga wanda ya yi aiyukan raya kasa irin sa ba “b azan iya lissafa ma ka irin aiyukan raya kasa da ya gudanar ba. Har yanzu ba wanda ya yi irin na shi amma ba mai magana ba ne”

Wasu Katsinawa ma da Babangida ya fara kirkiro mu su jiha a 1987 da Akwa Ibom sun nuna ba za su manta da tarihin ba.

Babangida wanda ya ce yanzu ya na shirin cika shekaru 84 a duniya ya yi fatan ko bayan ran sa dakin karatun sa ya amfani jama’a wajen binciken ilimi.

An tara biliyoyin Naira a wajen taron inda Abdulsamad Rabi’u ya ba da kaso mafi tsoka na Naira biliyan 5 sai Janar Theophilus Danjuma ya biyo baya da Naira biliyan 3.

Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84%
Next Post: IBB: Ba Shakka Abiola Ya Lashe Zaben Yuni 12

Karin Labarai Masu Alaka

Hadakar Gwamnatin Najeriya Da Amurka Ne Suka Kai Hari Sokoto Najeriya
An Gargaɗi Mazauna Maiduguri Su Guji Yaɗa Labaran Ƙarya Afrika
Jirgin Hakar Mai Daga Turkiyya Ya Isa Mugadishu Afrika
Shugaban Amurka Yace Zasu Kakabawa Mashigar Hormuz Takunkumi Afrika
Shugaba Tinubu Ya Tafi Kasar Faransa Afrika
NYSC – Sai An Gabatar Da Takardar NERD Kafin Shiga Bautar Ƙasa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Nijar: Zamu Tsananta Bincike A Bakin Iyakokin Mu Afrika
  • Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC Siyasa
  • Makiyaya Sun Shiga Matsala Sakamakon Fari A Kasar Kenya Afrika
  • Mutane 13 Sun Mutu Inda Wasu 57 Suka Jikkata A Barundi Afrika
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Afirka Ta Kudu Na Kokarin Kafa Wasu Dokoki A Kasar Labarai
  • Amurka Da Tarayyar Turai Sun Fidda Sanarwa Afrika
  • Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.