Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993
Published: October 19, 2025 at 3:12 AM | By: Newsdesk | Updated: November 16, 2025

Tsohon shugaban mulkin soja na Najeriya Janar Ibrahim Badamasi Babangida ya ce hakika marigayi Moshood Abiola ya lashe zaben watan Yuni na 1993 wanda gwamnatin sa ta soke.

Janar Babangida na magana ne a Abuja wajen taron kaddamar da littafin tarihin rayuwar sa ta aiki mai taken “A journey in service” da asusun gina dakin karatu na IBB a Minna.

“Na dau alhakin duk abun da gwamnati na ta gudanar, soke zaben 1993 na daga abubuwan da su ka zama masu tsauri a rayuwa ta” Inji Janar Babangida bayan tabbatar da cewa Abiola ya cika dukkan sharuddan lashe zaben wajen yawan kuri’a da kuma samun adadin yankuna.

Janar Babangida ya yabawa gwamnatin tsohon shugaba Buhari don aiyana Abiola a matsayin tsohon shugaban kasa duk da hakan ya faru bayan rayuwar sa.

Tsohon mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo da ya yi btar littafin mai shafi 420 a gaban mahalarta da su ka hada da shugaba Bola Tinubu da Janar Yakubu Gowon ya kawo bayanan yanda Babangida ya kwance damarar Dimka bayan kisan gilla ga Janar Murtala da kuma yanda juyin mulki ya kawo Buhari kan mulki a 1983 har sake juyin mulki a 1985 da Babangida ya hau da labarin su Janar Mamman Vatsa wanda a ka yankewa hukuncin kisa sanadiyyar shirin juyin mulki. Hakanan ya kawo lakabin Babangida da ya hada da MARADONA don yanda ba a gane matakin da zai dauka sai ya cimma nasara sai EVIL GENIUS da ke nuna hatsabibancin sa a aikin soja.

Janar Muhammad Barau mai ritaya ya ce ya yi aiki da Janar Babangida kuma har yau bai ga wanda ya yi aiyukan raya kasa irin sa ba “b azan iya lissafa ma ka irin aiyukan raya kasa da ya gudanar ba. Har yanzu ba wanda ya yi irin na shi amma ba mai magana ba ne”

Wasu Katsinawa ma da Babangida ya fara kirkiro mu su jiha a 1987 da Akwa Ibom sun nuna ba za su manta da tarihin ba.

Babangida wanda ya ce yanzu ya na shirin cika shekaru 84 a duniya ya yi fatan ko bayan ran sa dakin karatun sa ya amfani jama’a wajen binciken ilimi.

An tara biliyoyin Naira a wajen taron inda Abdulsamad Rabi’u ya ba da kaso mafi tsoka na Naira biliyan 5 sai Janar Theophilus Danjuma ya biyo baya da Naira biliyan 3.

Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84%
Next Post: IBB: Ba Shakka Abiola Ya Lashe Zaben Yuni 12

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar MDD Tace Wadanda Suka Mutu A Harin Sudan Sun Haura 70 Afrika
Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC Afrika
An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda Najeriya
Hadakar Gwamnatin Najeriya Da Amurka Ne Suka Kai Hari Sokoto Najeriya
Take Hakkin Dan Adam Zai Haifar Da Juyin Juya Hali A Najeriya Najeriya
Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
  • Shugaban Kasar Uganda Yana Kokarin Mayar Da Mulkin Kasar Na Gado Labarai
  • Fanny Amun Ya Yi Murabus A Matsayin Shugaban Kwamitin Binciken NFF Wasanni
  • Miliyan Biyar Ko Rayuwata: Barazanar ’Yan Ta’adda Ta Jefa Wani Mazaunin Dukku Cikin Fargaba Afrika
  • NEDC Ta Fara Shirin Kera Sanitary Pads A Gombe Domin Samar Da Sana’o’i Afrika
  • Shugaban Hukumar NAHCON Ya Ajeye Mukaminsa Labarai
  • Sojin Kasar Congo Da ‘Yan Tawaye Sun Kara Shiga Yankin Uvira Labarai
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Talata 11.18.2025 Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.