Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

‘Yan Sandan Jihar Bauchi Sun Kama Wasu Matasa da Ake Zargin Su Da Sara Suka 
Published: January 19, 2026 at 9:28 AM | By: Bala Hassan

Rundunan ‘Yan Sandan Jihar Bauchi Ta Kama ‘Yan Sara Suka

An Kama ‘Yan Ta’adda Goma Sha Huɗu (‘Yan Sara-suka) a lokacin wani samame a Bauchi.

Rundunan ta ‘yan sandan jihar Bauchi da ke arewa maso gabas a Najeriya tace a ranar 15 ga Janairu 2026 da misalin ƙarfe hudu da rabi na yammaci, wata sashin sintiri ta yi aiki na kai-kawo kan ayyukan ‘yan ta’adda (‘Yan Sara-suka) a anguwanin Bakaro, Kofar Dumi, Tudun Yarima da Karofin Madaki.

Bayan samun rahoton leken asiri na sirri, jami’in ‘yan sanda na ‘A’ Division Bauchi CSP Hassan A. Musa ya jagoranci wata tawaga da gaggawa inda ya ya cafke wadanda ake zargi da aikata wannan aika-aika, kamar yadda Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sandan jihar SP Nafiu Habib, ya bayyana a madadin kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi Sani Omolori Aliyu.

Wa’yanda aka kama sune.

1. Malam Abbati mai shekaru 20,

2. Malam Mamman mai shekaru 21,

3. Malam Adamu dan shekaru 22,

4. Malam Khalid mai shekaru 20,

5. Malam Abubakar mai shekaru 19,

6. Mr. Mahmood dan shekaru 22,

7. Malam Jabir mai shekaru 21,

8. Malam Haruna mai shekaru 18,

9. Malam Khalid mai shekaru 18,

10. Malam Abubakar dan shekaru 19,

11. Malam Kabiru mai shekaru 20,

12. Malam Anas mai shekaru 20,

13. Malam Mohammed dan shekaru 19,

14. Abdulkarim mai shekaru 22,

Duk kansu daga unguwar Kofar Dumi, Karofin Madaki, Tudun Yarima, da Bakaro, a Bauchi

Wadanda ake zargin sun amsa laifinsu na hada baki a tsakaninsu, inda suke dauke da makamai masu hatsarin gaske da suka hada da wukake masu kaifi, da makamantansu, inda suka mamaye yankunan suka kai musu hari da duka ga al’uma ma zauna unguwar da aka ambata, tare da kwace musu wayoyin hannu da kudi, sannan suka raunata duk wanda ya ki mika musu.

Kwamishinan ‘yan sanda, CP Sani-Omolori Aliyu, ya yabawa al’umar jihar Bauchi bisa hadin kai da goyon bayan da su ke bayarwa, wajan kawo rahoton bata gari, sannan ya karfafa musu gwiwa da su kasance masu taimaka wa jami’an tsaro wajan sanya ido ga masu aikata miyagun hali

Labarai

Post navigation

Previous Post: Kasar Sham Ta Sanar Da Tsagaita Wuta Tsakaninta Da Kungiyar Kurdawa
Next Post: Mutum Mafi Tsufa A Saudiyya Ya Rasu Yana Da Shekaru 142

Karin Labarai Masu Alaka

Babu Alamar Tsagaita Wuta A Yaki Da Akeyi Tsakanin Isra’ila Da Amurka Afrika
Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC Labarai
Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
Tattalin Arzikin Kasar Botswana Zai Farfado Afrika
Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado Amurka
Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Malami: “Da Gwamnatin Tarayya Na Daukar Shawara Da Ba’a Kai Inda Ake Ba” Najeriya
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Afrika
  • Ukraine Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Tsarin Cimma Yarjejeniya Sauran Duniya
  • Ko Arsenal Zata Iya Lashe Gasar Firimiya lig Na Bana Wasanni
  • Menene Illar Yada Labaran Karya A Kafofin Sada Zumunta Na Zamani Labarai
  • Kotu Ta Bada Belin Abubakar Malami Bisa Wasu Sharruda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
  • Yaki Ta Sararin Samaniya Ya Cigaba Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.