Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Shugaban Ukraine Ya Tattauna Da Trump Akan Zaman Lafiya
Published: December 27, 2025 at 5:48 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 27, 2025

Shugaban kasar Ukrain, Volodymr Zelensky yana so ya tattauna kan batutuwan da suka Shafi yankunan kasar da shugaban Amurka Donald Trump, wadanda su ne manyan abubuwa da suke kawo cikas wajen kawo karshen yakin ta da kasar Rasha.

Shugabannin biyu zasu tattauna ne a jihar Florida ranar Lahadi, a yayin da aka kusa karkare shirin zaman lafiya mai matakai ashirin, da kuma tabbatar da tsaro.

Da yake sanar wa da manema labarai kan batun tattaunawar, Zelensky ya ce za’a iya cimma matsaya da dama kafin zuwan sabuwar shekara, saboda fadar Washington ta zage dantse wajen ganin ta kawo karshen yaki gadan-gadan da Rasha ke yi da Ukrain, wanda ya kasance mafi muni a tarayyar turai tun bayan yakin duniya na biyu.

Israela ta kasance kasa ta farko da ta amince da Jamhuriyar Somaliland, da ta ayyana kan ta a matsayin kasa me cin gashin kan ta, ranar Jumu’a kuma wannan kuduri zai iya sauya fasalin dabi’un yankuna, kuma zai kawo kalubale ga ra’ayin Somalia na rashin son a warewa

Fira minista Benjamin Netanyahu, ya ce Israila zata nemi hadin guiwa da Somaliya a harkar noma, lafiya, fasaha da kuma tattalin arziki kuma a wani jawabi ya taya shugaban Somaliya Abdulrahman Muhammad Abdullahi murna, tare da yaba yadda yake gudanar da mulkin sa, ya kuma gayyace shi ya kai ziyara Israil.

Netanyahu ya ce wannan furuci, na daga cikin tsarin hadakar yankuna na Abraham Accords, wanda aka rattaba hannu a kai bisa ga shawara shugaba Donald Trump.

An kulla yarjejeniyar ne da aka tsara a shekarar 2020, lokacin mulkin Trump na farko, kuma ta kunshi kasar Isra’ila ta yi huldar diplomassiya bisa ka’ida da kasashen hadaddiyar daular larabawa, da Bahrain, tare da wasu kasashen da suka hadu daga baya.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda
Next Post: Najib Razak Zai Kara Shekaru 15 A Gidan Yari Saboda Cin Zarafin Kujerar Mulki

Karin Labarai Masu Alaka

Fafaroma Leo Zai Ziyarci Kasashen Afirka Amurka
Shugaba Donald Trump Yabada Umarnin Hana Jiragen Dakon Mai Shiga Venezuela Amurka
Yeriman Ingila Ya Mayarwa Trump Martani Amurka
Sakataren Harkokin Wajen Amurka Yace Rahoton Kasashe Biyar Akan Rasha Yana Dauke Da Damuwa Amurka
Iran Ta Karyata Tattaunawa Da Washington Afrika
Emmanuel Macron: Yakamata Wani Sashi Ya Rika Takawa Wani Sashi Birki A Tsarin Demokradiya Amurka Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi Afrika
  • Afrika Ta Kudu Ta Dora Haraji Mai Yawa Kan Karafa Afrika
  • Amurka Da Iran Zasu Tattauna A Kasar Oman Amurka
  • EFCC Ta Cafke Fitacciyar Jarumar Kannywood Samha Inuwa Labarai
  • Ranar Talata Amurka Da Isra’ila Sun Cigaban Da Kai Farmaki Iran Afrika
  • Kasar Chadi Ta Rufe Iyakar Ta Da Kasar Sudan Afrika
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana Afrika
  • Gwamnatin Afirka Ta Kudu Na Kokarin Kafa Wasu Dokoki A Kasar Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.