Kwana daya da fara hana jiragen ruwa shiga ko fita daga tashoshin ruwan Iran, dakarun Amurka suka ce babu jirgin ruwa ko daya daya tsallake shinge da suka kafa, jiragen ruwa shida sun bi umarni suka juya, wannan shine bayani na farko da aka samu tun bayan da shugaban Amurka Donald trump, ya bada umarnin killace tashoshin ruwan Iran, sakamakon rushewar zaman shawarwari da kasashen biyu suka yi a Pakistan.
Sojojin na Amurka suka ce wannan mataki ya shafi jirage ne da suke kokarin shiga tashoshi a gaban ruwan Iran da Oman.
Rundunar mayakan na Amurka ta ce fiye da sojojin Amurka dubu 10, jiragen yaki na ruwa masu yawa da masu tashi sama ne suke aiwatar da dokar hana zirga zirga zuwa tashoshin ruwan na Farisa.
Sanarwar da cibiyar kula da yake yake ta Amurka ta bayar tace dokar ta shafi dukkan jiragen ruwa daga ko wace kasa ba tare da wani zabi ba.
Sanarwar ta ci gaba da cewa hana zirga zirgar zai shafi illahirin tashoshin ruwan Iran, amma za’a kyale jirage dauke kayan abinci, magunguna da wasu muhimman kayayyaki su wuce bayan da aka duba abunda suke dauke dashi.
Masana sun gayawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa matakin yana iya janyo martani daga Iran, da zai iya kara dagula lamari kan yarjejeniyar tsagaita wuta maras tabbas.


