Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa
Published: April 14, 2026 at 8:43 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kwana daya da fara hana jiragen ruwa shiga ko fita daga tashoshin ruwan Iran, dakarun Amurka suka ce babu jirgin ruwa ko daya daya tsallake shinge da suka kafa, jiragen ruwa shida sun bi umarni suka juya, wannan shine bayani na farko da aka samu tun bayan da shugaban Amurka Donald trump, ya bada umarnin killace tashoshin ruwan Iran, sakamakon rushewar zaman shawarwari da kasashen biyu suka yi a Pakistan.

Sojojin na Amurka suka ce wannan mataki ya shafi jirage ne da suke kokarin shiga tashoshi a gaban ruwan Iran da Oman.

Rundunar mayakan na Amurka ta ce fiye da sojojin Amurka dubu 10, jiragen yaki na ruwa masu yawa da masu tashi sama ne suke aiwatar da dokar hana zirga zirga zuwa tashoshin ruwan na Farisa.

Sanarwar da cibiyar kula da yake yake ta Amurka ta bayar tace dokar ta shafi dukkan jiragen ruwa daga ko wace kasa ba tare da wani zabi ba.

Sanarwar ta ci gaba da cewa hana zirga zirgar zai shafi illahirin tashoshin ruwan Iran, amma za’a kyale jirage dauke kayan abinci, magunguna da wasu muhimman kayayyaki su wuce bayan da aka duba abunda suke dauke dashi.

Masana sun gayawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa matakin yana iya janyo martani daga Iran, da zai iya kara dagula lamari kan yarjejeniyar tsagaita wuta maras tabbas.

Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli
Next Post: Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Amurka Yayi Barazanar Kulle Wani Dan Jarida Amurka
Aisha Buhari Ta Bayyana Irin Kalubalen Da Ta Fiskanta Sakamakon Biyewa Jita-Jita Labarai
Makokin Ashura: An Gudanar Da Taron Tunawa Da Aliyul Asghar A Gombe Afrika
Barayin Waya Sun Yanke Yatsun Hannu Guda Biyu Da Gefen Kunne A Bauchi Labarai
Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
Limamin Da Ya Ceci Kiristoci Lokacin Rikicin Addini A Jihar Filato Ya Rasu Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Soyinka Ya soki Yawan Jami’an Tsaron Da Ake Bai Wa Seyi Tinubu Najeriya
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Damara Ya Tallafa Wa Gasar Karatun Al-Qur’ani Da Naira Miliyan Biyar A Bambam Afrika
  • Kasar Amurka Takara Saka Takunkumi Akan Kasar Venezuela Amurka
  • Shugaban Hukumar Hana Yaduwar Cututtuka A Afirka Yace Akwai Rashin Fahimta A Tsakanin Kasashen Da Amurka Take Tallafawa Afrika
  • Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci Afrika
  • Wani Bincike Ya Nuna Cewar Da Wuya Iran Ta Bude Mashigin Hormuz Afrika
  • Kasar China Ta Kaddamar Da Rawar Daji A Yankin Taiwan Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.