Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Hadakar Ta Da Amurka Wajen Yakar ‘Yan Ta’adda
Published: December 27, 2025 at 5:38 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ta hanyar amincewa da hadin guiwa da kasar Amurka a bainar jama’a, kan harin da Amurkan ta kai ranar kirsimeti, Nigeria ta tsallake rijiya da baya wajen fuskantar harin sojin Amurka kai tsaye, wanda shugaba Donald Trump ya yi barazanar kaiwa wata daya da ya wuce.

Amma masana harkar tsaro sun ce babu tabbacin ko irin waddannan hare-hare zasu iya maganin ‘yan ta’adda da suka dade suna barazana ga mutanen yankin

Trump ya fada a shafin sa na Truth Social ranar Alhamis cewa dakarun Amurka sun kai farmaki ga kungiyar ‘yan ta’adda a arewa maso gabashin Nigeria, bayan da gwamnatin Nigeria ta bukaci hakan, ya ce ‘yan ta’addan suna cin zarafin mabiya addinin kirista.

Ranar Jumu’a Trump ya ce harin da sojan Amurkan suka kaiwa ‘yan ta’adda da, da farko ranar Laraba ya kamata a kai shi, amma sai ya ce a dakata sai washegari.

Wani jami’in tsaron Amurka da ya nemi a boye sunan sa, ya shaidawa kamfanin dillacin labarai na Reuters cewa An yi amfani da makamai masu linzami na Tomahawk ne, wanda aka harbo su daga jirgin ruwan yakin Amurka a tekun Guinea.

Fadar gwamnatin Nigeria a Abuja ta tabbatar da yarjewar ta ga kai harin, kamar yadda ministan harkokin kasashen waje Yusuf Tuggar ya fada ranar Jumu’a, cewa harin na hadin guiwa ne, kuma bashi da alaka da wani yanki.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Hadakar Gwamnatin Najeriya Da Amurka Ne Suka Kai Hari Sokoto
Next Post: Shugaban Ukraine Ya Tattauna Da Trump Akan Zaman Lafiya

Karin Labarai Masu Alaka

Gobara Ta Tashi A Makarantar Koyon Jinyar Dabbobi Dake Jihar Kano Najeriya
Yan Najeriya na ci gaba da maida martani akan sabuwar dokar zabe da majalisar Dattawan kasar ta Amince dashi Najeriya
Wata Biyu Najeriya Bata Bada Lasisin Shigo Da Mai Daga Ketare Ba Labarai
Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Bola Tinubu Ta Raba Taraktoci Dubu Biyu Domin Inganta Noma Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Kawo Cikas Ga Cinikin Nama A Kenya
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa
  • Shugaba Trump Yace Amurka Takai Hari Kharg Tsibiri a Kasar Iran
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan
  • Jami’ai A Afirka Sunce Tashin Farashin Mai Kalubale Ne Ga Tattalin Arziki

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
  • Zamu Hana Wasu ‘Yan-Najeriya Visa Shiga Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa Labarai
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC Siyasa
  • Akalla Mutane 8 Sun Mutu Biyo Bayan Bindiga Da Wata Tanka Tayi Afrika
  • Gwamnan Neja Bago Na Cin Zarafin Talakawan Da Suka Zabe Shi Labarai
  • Kamfanin Hakar Ma’adanai Na Kasar Kanada Ya Cigaban Da Aikinsa Labarai
  • Jirage Marasa Matuka Sun Kaiwa Jiragen Ruwan Mai Hari A Gulf Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.