Shugaban farko na Hukumar Tsarin Bayanan Ƙasa ta jihar Gombe (Gombe Geographic Information Systems – GOGIS), Dr. Kabiru Usman Hassan, ya bayyana manyan sauye-sauyen da hukumar ta samu cikin shekaru shida da ya jagorance ta, yayin da wa’adin aikinsa ya zo ƙarshe.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar ƙarewar wa’adinsa, Dr. Hassan ya ce kafa GOGIS ba wai don samar da sabuwar hukuma kawai ba ne, illa don gina cibiyar da za ta inganta gudanar da harkokin filaye ta hanyar amfani da fasaha, gaskiya, ƙwarewa da ingantaccen tsarin gudanarwa.
Ya ce da goyon bayan Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, hukumar ta aiwatar da muhimman sauye-sauye na doka, manufofi, fasaha da tsarin gudanarwa, waɗanda suka sauya yadda ake gudanar da harkokin filaye a jihar.
A cewarsa, daga cikin manyan nasarorin da aka samu akwai kafa cibiyar gudanarwa ta zamani, gina cibiyar ba da hidima ta dindindin, mayar da dubban bayanan filaye zuwa tsarin na’ura mai kwakwalwa, ƙaddamar da Takardun Mallakar Filaye (Certificate of Occupancy) na zamani, inganta taswirar ƙasa ta hanyar fasahar geospatial, ƙarfafa tsarin tsara birane da kuma haɓaka kuɗaɗen shiga na cikin gida zuwa sama da Naira biliyan 7.5.
Dr. Hassan ya ce nasarorin da aka samu ba nasa kaɗai ba ne, illa sakamakon haɗin gwiwar ma’aikatan GOGIS da sauran masu ruwa da tsaki.
Ya gode wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya bisa amincewar da ya ba shi da kuma irin damar da ya bai wa ƙwararru wajen gudanar da ayyukansu cikin bin doka, ko da kuwa wasu matakan da aka ɗauka sun kasance masu wahala ko suka fuskanci suka.
Hakazalika, ya yabawa ma’aikatan GOGIS saboda jajircewa, ƙwarewa da sadaukarwar da suka nuna wajen tabbatar da nasarar sauye-sauyen da aka aiwatar.
Ya kuma miƙa godiyarsa ga hukumomin gwamnati, cibiyoyin ƙwararru, sarakunan gargajiya, abokan hulɗar ci gaba, hukumomin tsaro, masu zuba jari da al’ummar Jihar Gombe bisa irin gudunmawar da suka bayar wajen ci gaban hukumar.
Sai dai Dr. Hassan ya bayyana cewa aiwatar da gyare-gyaren bai rasa ƙalubale ba, inda ya ce sun fuskanci turjiya daga wasu sassa, matsalolin shari’a, ƙalubalen gudanarwa, rashin fahimta daga jama’a da kuma barazanar kai tsaye ga wasu jami’ai.
Duk da haka, ya ce waɗannan ƙalubalen sun ƙara tabbatar masa da cewa dorewar sauyi na buƙatar jajircewa, gaskiya, riƙon amana da sadaukar da kai domin amfanin al’umma.
Ya kuma amince cewa duk da nasarorin da aka samu, an yi wasu kura-kurai, wasu matakai sun fuskanci suka, yayin da wasu manufofi suka buƙaci ƙarin lokaci kafin a cimma su.
Dr. Hassan ya jaddada cewa babban abin da ya kamata jami’an gwamnati su bari a baya ba gine-ginen mutum ba ne, sai dai ƙarfafa cibiyoyi masu ɗorewa, inganta tsarin mulki da kuma shimfiɗa tubalin da magajansu za su gina a kai.
A ƙarshe, ya bayyana cewa yana barin muƙaminsa cikin godiya da alfahari kan irin tubalin da aka aza, tare da bayyana fatan cewa GOGIS za ta ci gaba da kasancewa abin koyi a fannin gudanar da harkokin filaye cikin gaskiya da amfani da fasahar zamani a Najeriya.


