Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Kasar Guinea Ta Soke Wasu Jam’iyyun Siyasa
Published: March 9, 2026 at 6:31 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin kasar Guinea ta soke jam’iyyun siyasa 40 a kasar, inda ta ce a wata doka da ta wanzar ranar Jumu’a za’a rufe duk manya da kananan ofisoshin jam’iyyun 40 a fadin kasar, kuma za’a haramta musu amfani da duk wata alama ko zane dake nuni jam’iyyar.

Dokar ta ce jam’iyyun sun kasa sauke hakkin doka, kamar aikewa da bayanan kudaden su. Da yawa daga cikin jam’iyyun sun koka da wannan hukunci, inda suka dage akan sun yi duk wani abu da doka ta tanada.

Babban dan jam’iyyar adawa a kasar ya ce turjiya kai tsaye ga shugaban kasar mai ci a yanzu ita ce kadai hanyar da za’a kawo sauyi.

Shugaba Mamady Doumbouya, wanda da soja ne, yayi juyin mulki a shekarar 2021, daga baya kuma ya ci zabe na zama shugaban kasa har zuwa shekaru 7 a watan Disamba, wanda sauran ‘yan takara suka kalubalanta. Ana sa ran yin zaben ‘yan majalisar dokokin kasar a watan Mayu.

Afrika, Labarai, Siyasa

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Sojoji Da Fararen Hula A Arewa Maso Gabashin Najeriya
Next Post: Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa

Karin Labarai Masu Alaka

Sojojin Kasar Uganda Sun Bazama Neman Bobi Wine Sakamakon Rikicin Bayan Zabe Siyasa
“Yan Wasan Super Eagles Sun Karbi Alkawarin Da Gwamnati Tayi Musu AFCON 2023 Labarai
China Ta Yi Kira Da Kasashen Gabas Ta Tsakiya Su Hada Kai Labarai
Iran Tabada Tabbacin Cigaba Da Rufe Mashigar Hormuz Afrika
Rasha Takai Mummunan Hari Birnin Kyiv Afrika
Jami’an Tsaro Suna Farautar Wasu ‘Yan Ta’adda A Najeriya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz
  • Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026
  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Afirka Ta Kudu Zata Fuskanci Koma Baya A Bangaren Samar Da Ayyukanyi Afrika
  • Aikin Layin Dogon Kasar Uganda Zai Hade Kasar Da Tanzania Da Kwango Kimiya
  • Kasar Iceland Ta Kauracewa Bikin Gasar Wakokin Shekara Mai Zuwa Labarai
  • Hukumar EFCC Ta Kwace Gidan Tsohon Antoni Janar Abubakar Malami Najeriya
  • Tinubu Ya Bayyana ‘Yan Bindiga Da Cewa Ruwa Yakarewa Dan Kada Afrika
  • Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
  • Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai
  • Yawan Mai Da Kasashen OPEC Suke Hakawo Yayi Kasa Sosai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.