Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika

Gwamnatin Sham Tace Harin Kurdawa Ya Hallaka Sojojin Kasar
Published: January 21, 2026 at 9:36 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin kasar Sham ta ce harin da kungiyar ‘yan tawayen kurdawa ta SDF ta kai wa dakarun ta da jiragen drone ya yi sanadiyar hallaka sojoji 7 ranar laraba duk da kungiyar SDF din sun musanta hakan.

Wannan abu na barazanar kawo koma baya ga yarjejeniyar tsagaita wuta da bangarorin biyu suka kulla, bayan da suka shafe kwanaki suna gwabza kazamin fada.

Sojin Sham sun ce, wannan harin da aka kai yayin da dakarun nasu ke neman killace wani sansanin sojoji da aka kame mai dauke da bama bamai, tunzura ce me hadari.

Kungiyar ta SDF ta ce bata kai hari ba, ta ce an samu fashewar bama bamai ne lokacin da sojojin Sham ke kokarin matsar su. Ta kuma zargi sojojin na Sham da karya alkawarin yarjejeniyar zaman lafiya hanyar kai hare-hare a wurare da dama.

Bayan shafe kwanaki tana ci gaba da samun nasara, gwamnatin Sham ta ce ran Talata, ta cimma fahimta tsakanin ta da dakarun SDF, don yarda da yarjejeniyar tsagaita wuta na kwana hudu, kuma su yarda su kasance karkashin mulkin gwamnatin, ko kuma a ci gaba da kai musu farmaki a birane biyu da suka rage musu da suke rike da madafun iko.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Harin Jirgi Maras Matuki Ya Hallaka Mutane A Sudan
Next Post: ‘Yan Kasar Venuzuela Zasu Fara Komawa Gida

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Amurka Da Rasha Zasu Kawo Karshen Tsagaita Nukiliya Amurka
Pantami Ya Bayyana Dalilin Mayar Da Zaben Sa Abuja Afrika
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos Afrika
Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika
Jami’ai Daga Amurka Sunce Yakin Amurka Da Iran Zaizo Karshe Amurka
Jami’an Diflomasiyyar Iran Dana Amurka Sun Tattauna A Kasar Oman Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • Tattalin Arzikin Kasar Bahrain Ya Bunkasa Sakamakon Ruruwar Masu Yawon Bude Ido Labarai
  • Fadar Shugaban Kasa Ta Karyata Jita-Jitar Yunkurin Sanya Wa Tinubu Guba A Abinci Afrika
  • Ministan Kudin Botswana Yace Akwai Hasashen Cewa Tattalin Arzikin Kasar Zai Ragu Amurka
  • Fafaroma Leo Zai Ziyarci Kasashen Afirka Amurka
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya Afrika
  • Shugaban Amurka Yace Zasu Kakabawa Mashigar Hormuz Takunkumi Afrika
  • GTA Hausa Logo
    Shirin Dare 2030 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.