Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaba Trump Ya Bukaci Kasar Iran Ta Mika Wuya
Published: March 6, 2026 at 9:53 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Amurka Donald Trump ya bukaci kasar Iran ta mika wuya kai tsaye a ranar Jumu’a, bayan da aka shafe mako daya ana artabun musayar makamai tun bayan da Amurka da Isara’ila suka kaiwa Iran harin ana tsaka da tattaunawar cimma yarjejeniya kan makaman nukiliya na Iran din. Wannan furuci na Trump zai sa sulhun kawo karshen yakin yayi wahala.

Trump ya wallafa bukatar a shafin sada zumunta, bayan da shugaban kasar Iran ya sanar cewa wasu kasashe da ba’a bayyana sunan su ba sun fara shiga tsakani domin kawo sulhu, wannan shine alama ta farko na yunkurin diplomasiyya wajen kawo Karshen yakin.

A wallafawar tasa Trump ya ce ba wata tattaunawar sulhu da za’a yi da Iran, face mika wuya kai tsaye. Wannan furuci da ake ganin zai iya dagula al’amura maimakon ya gyara su, ya kawo tsaiko kan shige da ficen makamashi a duniya, ya kuma dagulawa kasuwannin hannun jari lissafi, inda kasuwannin a Turai da kuma Wall Street na Amurka suka tafka asara da budewar su ranar juma’a.

Amurka, Labarai, Sauran Duniya, Siyasa, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Shugaban Najeriya Tinubu Ya Amince Na Tura Jakadu
Next Post: Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Zata Shigar Da Lebanon Cikin Cimma Yarjejeniya Afrika
Shugabannin Darikar Anglican Sun Bada Sanarwar Kafa Sabuwar Majalisa Afrika
Farashin Gangar Mai Yayi Gagarumar Fadi A Kasashen Duniya Labarai
Shugaba Donald Trump Ya Nada Shugaban Bankin Tarayya Amurka
Kasar Spain Ta Rufe Sararin Saman Kasar Amurka
Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz
  • Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026
  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Kasar Guinea Ta Soke Wasu Jam’iyyun Siyasa Afrika
  • Fitaccen Dan Jarida a Sokoto Surajo Dalhatu Sifawa Ya Rasu Najeriya
  • Amurka Ta Janye Sojojinta Daga Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Amurka Da Iran Sun Tattauna A Kasar Pakistan Afrika
  • Iran Ta Harbo Jiragen Yakin Amurka Biyu Amurka
  • Ukraine Da Syria Zasuyi Haɗin Gwiwar Tsaro Labarai
  • Shugaba Trump Yayi Barazanar Tarwatsa Cibiyar Makamashin Iran Amurka
  • Sojin Ukraine Sun Janye Daga Gabashin Kasar Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.