Shugaban Amurka Donald Trump ya bukaci kasar Iran ta mika wuya kai tsaye a ranar Jumu’a, bayan da aka shafe mako daya ana artabun musayar makamai tun bayan da Amurka da Isara’ila suka kaiwa Iran harin ana tsaka da tattaunawar cimma yarjejeniya kan makaman nukiliya na Iran din. Wannan furuci na Trump zai sa sulhun kawo karshen yakin yayi wahala.
Trump ya wallafa bukatar a shafin sada zumunta, bayan da shugaban kasar Iran ya sanar cewa wasu kasashe da ba’a bayyana sunan su ba sun fara shiga tsakani domin kawo sulhu, wannan shine alama ta farko na yunkurin diplomasiyya wajen kawo Karshen yakin.
A wallafawar tasa Trump ya ce ba wata tattaunawar sulhu da za’a yi da Iran, face mika wuya kai tsaye. Wannan furuci da ake ganin zai iya dagula al’amura maimakon ya gyara su, ya kawo tsaiko kan shige da ficen makamashi a duniya, ya kuma dagulawa kasuwannin hannun jari lissafi, inda kasuwannin a Turai da kuma Wall Street na Amurka suka tafka asara da budewar su ranar juma’a.


