Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Mayakan Boko Haram Da ISWAP Sun Kai Hari Cikin Dare
Published: April 10, 2026 at 9:50 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A Najeriya gamayyar mayakan kungiyar Boko Harama da ISWAP sun kai hari na hadin baki cikin dare kan sansanoni daban daban a jihar Barno, har suka kashe wani janar da wasu sojojin kasar, kamar yadda wasu majiyoyin soji suka fada ranar Ahamis.

Helkwatar mayakan kasar, sunce mayakan sun kai hari kan wata cibiyar sojoji da ke Benisheikh amma aka taka musu birki, ta tabbatar da an kashe sojoji a artabun, helkawatar ta bukaci jama’a su dakaci karin bayani dangane da wadanda rikicin ya shafa.

Mayakan sun fara kai hari ne kan garuruwan Pulka, da Bakin ruwa wadanda suke karamar hukumar Gwoza a daren laraba, sannan suka yi kokarin kama helkwatar runduna ta musamman ta 29 dake Benisheikh da tsakar dare, inji helkwatar ta mayakan Najeriya. Ta kara da cewa sojojin Najeriya suka ja daga karkashin jagorancin janar Oseni Braimah suka fatattaki ‘yan bindigar.

Sai dai wasu majiyoyin soja biyu sun fadawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa, ‘yan bindigar sunyi dai dai da sansanin da yake Benisheikh, suka kashe janar Oseni Braimah, da wasu sojoji cikin su har da wani mai mukamin keftin, suka lalata motocin soja masu yawa. Kamfanin dillancin labarai na Reuters bashi da tabbaciin wannan labari.

Wani jami’in soja, wanda yana daga cikin wadanda suka kai dauki a Benisheikh, yace jiragen yaki ta sama su suka yi jigilar wadanda suka kwanta dama a harin na Benisheikh a ranar Alhamis, bayanda suka taimaka wajen korar ‘yan binidgar wadanda suka yi sa’o’I uku suna barna a yankin.

Ahalinda ake ciki kuma, rassan kungiyoyin al-qeada da ISIS a yammacin Afirka a karon farko sun baiwa hamata iska a Nijar, kamar yadda wata sanarwa da daya daga cikin kungiyoyin ta bayar, mataki a masu fashin baki suka ce ya karfafa gababar da take tsakanin kungiyoyin na shekara da shekaru.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Birtaniya Zata Hana Jiragen Ruwan Rasha Wucewa
Next Post: Kasuwannin Hannun Jari Sun Farfado

Karin Labarai Masu Alaka

Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara Labarai
Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Katsina Afrika
Farashin Mai Yana Cigaba Da Karuwa Afrika
Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Shirya Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Jihar Filato Afrika
Shugaba Tinubu Ya Turawa Majalisa Sunayen Mutane Biyun Da Zasu Shugabanci Sashin Albarkatun Mai Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ECOWAS Ta Saka Dokar Ta Baci A Afrika Ta Yamma Afrika
  • Jihar Gombe Ta Saka Hannu Kan Yarjejeniya Da Kamfanonin Tunisiya Kimiya
  • Gwamnatin Trump Ta Karawa Iran Wasu Takunkumai Amurka
  • Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi Labarai
  • An Yaba Wa Gwamnatin Bauchi Bisa Karban Bakuncin Gasar Polo Wasanni
  • Gombe Ta Yi Gasar Makarantun Firamare Don Bikin Cika Shekaru 100 Na Hassan Central Afrika
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutu Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.