Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026 Afrika
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola Afrika
  • ‘Yan Sandan Gombe Sun Fara Kama Motocin Da Ba Su Da Lambar Rajista ko Masu Boye Lambobinsu Afrika

Jirgi Marar Matuka Yayi Luguden Wutan A Abu Dhabi
Published: March 2, 2026 at 8:35 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wani jirgi mara matuki da ya tarwatse ya lalata wani katafaren ginin a birnin Abu Dhabi dake kusa da ofishin jakadancin Isra’ila da wasu ofisoshin jakadanci na kasa da kasa da dama, lamarin da ya haddasa kananan raunuka ga wata mata da yaronta, kamar yadda ofishin yada labarai na gwamnatin Abu Dhabi ya sanar da yammacin ranar Lahadi.

tarkacen jirgin mara matuki sun fado a gaban wani ginin Etihad Towers, bayan wata na’ura ta hana makamin fashewa a kasa, in ji ofishin yada labaran.

Bayan da Amurka da Isra’ila suka kaddamar da hare-hare kan Iran a ranar Asabar, Iran ta ce za ta kai hari kan sansanonin Amurka da ke yankin. Amma kuma ta afkawa yankuna da dama na farar hula da na kasuwanci a duk fadin garuruwan yankin Gulf, lamarin da ke kara fadada tasirin rikicin kan muhimman cibiyoyin zirga-zirgar jiragen sama da na kasuwanci a yankin.

Yayin da hare-haren ramuwar gayya ke ci gaba da yaduwa a jiya Lahadin, sun sake yin kaca-kaca a sassan kasashen Larabawa na yankin Gulf, inda aka ji karar fashewar abubuwa masu karfi a Dubai da Doha babban birnin Qatar da kuma Oman a karon farko.

Sanarwar da ofishin yada labaran gwamnatin Dubai data fitar ta ce, a birnin Dubai, wasu mutane biyu sun jikkata bayan da wasu tarkacen jiragen sama marasa matuka suka fado kan gidaje biyu lokacin da aka kama su.

Afrika, Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
Next Post: Isra’ila Takai Sabon Hari Tehran Ranar Lahadi

Karin Labarai Masu Alaka

Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka Afrika
‘Yan Bindiga A Mali Sun Kashe Direbobin Manyan Motoci Afrika
Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
Shugabannin Kiristoci Sun Taya Musulmi Murnar Sallah Domin Ƙarfafa Zaman Lafiya Afrika
Kasar Morocco Ta Kwashe ‘Yan Kasar Daga Sassan Ambaliyar Ruwa Afrika
Rikicin Gabas Ta Tsakiya Yanuna Alakar Kasashen Da Najeriya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar
  • Sakon Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu A Ranar Dimokraɗiyya Ta 2026
  • Za’a Bude Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Duniya 2026
  • Uefa Ta Zabi Artan, Ya Jagoranci Wasan Cin Kofin Uefa Super Cup
  • Shugaba Tinubu Ya Kafa Kwamitin Gaggawa Akan Cutar Ebola

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar NDLEA Ta Kama Miyagun Kwayoyi A Edo Afrika
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Ware Kudade Domin Bunkasa Rayuwar ‘Yan Najeriya Afrika
  • Ministan Harkokin Wajen Rasha Dana Iran Sun Tattauna Don Kawo Karshen Yaki A Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland Wasanni
  • Iran Da Amurka Zasu Cimma Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Cin Karensu Babu Babbaka A Najeriya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.