Rundunar ‘Yan Sandan jihar Gombe a Najeriya ta karɓi bakuncin Mataimakin Sufeto Janar na ‘Yan Sanda mai kula da shiyya ta 12 (Zone 12), AIG Vungmoh S. M. Kwaimo, a wata ziyarar aiki da nufin ƙarfafa haɗin gwiwa tare da zaburar da jami’an ‘yan sanda su ƙara himma wajen yaƙi da aikata laifuka da ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas.
Taron, wanda ya gudana a Hedikwatar Rundunar ‘Yan Sandan jihar Gombe, ya haɗa manyan jami’an ‘yan sanda daga sassa daban-daban na jihar da kuma mambobin Kwamitin Hulɗa Tsakanin ‘Yan Sanda da Al’umma (PPRC).
An gudanar da laccoci da tattaunawa domin ƙara ƙwarewar aiki, inganta ayyukan jami’an tsaro da kuma ƙarfafa matakan tabbatar da tsaro a yankin.
A jawabinsa na maraba, Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Gombe, CP Ahmed Umar Chuso, ya gode wa AIG Kwaimo bisa ziyarar tare da sake jaddada cikakken biyayya da ƙudirin rundunar na ci gaba da gudanar da aikinta bisa manufofin Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya.

CP Chuso ya bayyana irin nasarorin da rundunar ta samu wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a jihar Gombe, yana mai cewa ci gaba da tattaunawa da jami’ai da ƙarfafa haɗin gwiwa na taka muhimmiyar rawa wajen ɗaga ƙwarin gwiwa, tabbatar da ladabtarwa da kuma inganta gudanar da ayyukan da kundin tsarin mulki ya ɗora wa rundunar.
A nasa jawabin, Mataimakin Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, AIG Vungmoh Kwaimo, ya bayyana gamsuwarsa da yadda Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe ke gudanar da ayyukanta ƙarƙashin jagorancin CP Ahmed Umar Chuso.

Ya yaba da nasarorin da rundunar ta samu da kuma zaman lafiyar da ake morewa a jihar, tare da ƙarfafa jami’ai da su ci gaba da jajircewa domin dorewar waɗannan nasarori.
AIG Kwaimo ya bayyana cewa ziyarar ta Gombe ta biyo bayan irin wannan rangadin duba ayyukan runduna da ya gudanar a Jihar Bauchi.
Ya ce manufar rangadin ita ce tantance yadda ake gudanar da ayyukan ‘yan sanda a dukkan jihohin da ke ƙarƙashin Zone 12, sauraron ƙalubalen jami’ai da kuma samar da mafita ta hanyar tattaunawa mai ma’ana domin ƙara inganta ayyukan tsaro da ci gaba da aiwatar da manufar rundunar ta rashin sassauci ga masu aikata laifuka da ta’addanci.
Haka kuma, AIG Kwaimo ya yabawa Sufeto Janar na ‘Yan Sandan Najeriya, IGP Olatunji Rilwan Disu, bisa ƙoƙarin da yake yi wajen inganta jin daɗin jami’an rundunar.
Ya ce sauye-sauyen da IGP ya kawo sun fara haifar da sakamako mai kyau, sannan ya buƙaci jami’an da su rama wannan kulawa ta hanyar nuna cikakken biyayya, jajircewa, ƙwarewa a aiki da kuma yi wa ƙasa hidima ba tare da son kai ba.


