Mutane uku sun rasa rayukansu sakamakon mamakon ruwan sama mai ƙarfi tare da iska da ta afku a wasu sassan jihar Yobe dake arewa maso Gabashin Najeriya cikin dare, lamarin da ya haddasa mummunar barna ga gidaje da kadarori.
Ruwan saman da iskar sun shafi unguwannin Tsohon Nguru, Filin Idi da sauran yankuna, inda gidaje, shaguna, rumfunan kasuwa da katanga suka rushe ko suka lalace.
Rahotanni sun tabbatar da mutuwar mutane uku, yayin da daruruwan mazauna yankunan da abin ya shafa suka rasa matsugunansu sakamakon barnar da ruwan saman da iskar suka yi.
Wani mazaunin yankin, Bukar Adamu, ya ce iyalan da iftila’in ya shafa sun nemi mafaka a gidajen ‘yan uwa da kuma wasu gine-ginen gwamnati bayan gidajensu sun rushe.
Shi ma wani mazaunin yankin, Mustapha Modu, ya bayyana cewa iska mai ƙarfi ta kwashe rufin gidansa. Ya kuma ce wani ƙaramin yaro mai suna Ilya Alhassan ya rasu bayan ɗaki ya rufta a kansa a unguwar Filin Idi.
Mazauna yankunan sun yi kira ga gwamnati da ƙungiyoyin agaji da su gaggauta kai musu ɗauki tare da samar da kayan agaji ga iyalan da iftila’in ya shafa.


