Kungiyoyin ƙwadago na Najeriya (NLC) sun bukaci Gwamnatin kasar ta gaggauta sake duba mafi ƙarancin albashin ma’aikata na ƙasa wanda a halin yanzu yake kan ₦70,000, suna masu cewa ya daina dacewa da halin tsadar rayuwa da hauhawar farashin kayayyaki.
Shugaban NLC, Joe Ajaero, ya bayyana cewa hauhawar farashin abinci, sufuri, gidaje da sauran muhimman buƙatun rayuwa ya sa albashin na ₦70,000 ya zama ba zai iya biyan bukatun ma’aikaci ba.
Ƙungiyar ta ce za ta fara sabon tattaunawa da Gwamnatin Tarayya domin a samar da sabon mafi ƙarancin albashi da zai dace da halin tattalin arzikin ƙasar.
NLC ta jaddada cewa inganta walwalar ma’aikata na da muhimmanci wajen ƙara ƙwazo da ingancin aiki, tare da kira ga gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki su gaggauta ɗaukar matakin sake duba tsarin albashin Kasar


