Kasar Pakistan zata karbi bakuncin kasashen Saudiyya, Turkiyya da Masar a gobe Lahadi a fadar gwamnatin Islamabad don tattaunawa kan yakin Iran, yayin da Pakistan ta saka kan ta a matsayin jakadan sulhu don cimma yarjejeniya tsakanin Amurka da Iran kan kawo karshen yakin da aka yi wata daya ana tafkawa.
Ministocin harkokin waje na kasashen hudu, zasu yi tattaunawa mai zurfi kan abubuwa da suka kunshi shawo kan tashin hankali a yankin, a ganawar da zasu shafe kwanaki biyu suna yi a cewar ma’aikatar harkokin kasashen waje ta Pakistan a yau Asabar.
Ministan harkokin kasashen wajen na Turkiyya, Hakan Fidan, yace ganawar tasu zata nemi hanyar da za’a bi don kawo sulhu.
Kasashen hudu sun kasance wadanda ke kokarin sasantawa tsakanin fadar Washington da fadar Tehran, a yakin da Amurka da Isra’ila suka farwa Iran ranar 28 ga Watan Fabrairu.


