Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Ministan Harkokin Wajen Najeriya Yayi Murabus
Published: March 30, 2026 at 3:49 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ministan harkokin wajen Najeriya, Ambasada Yusuf Tuggar, ya yi murabus daga mukaminsa domin neman tsayawa takarar gwamna.

An bayyana hakan ne a ranar Litinin cikin wata takaitacciyar sanarwa da mai magana da yawun ma’aikatar harkokin waje, Kimiebi Ebienfa, ya fitar.

Ya ce, “An tabbatar da murabus din mai girma Ministan Harkokin Waje.”

Rahotanni sun nuna cewa Tuggar na daga cikin ministoci hudu a gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ake sa ran za su sauka daga mukamansu domin yin takara.

Tun da farko, mai ba ministan shawara kan harkokin yada labarai da dabarun sadarwa, Alkasim Abdulkadir, ya tabbatar da cewa Tuggar na da sha’awar tsayawa takarar gwamnan Jihar Bauchi.

A cewarsa, “Ministan yana da burin tsayawa takarar gwamnan Jihar Bauchi a zabe mai zuwa.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Hukumar Hasashen Kasuwanci Na Zargin Saida Bayanan Sirri
Next Post: Zulum Ya Rushe Majalisar Zartarwa Ta Jihar Borno

Karin Labarai Masu Alaka

An Kaddamar Da Jigilar Maniyyata Aikin Hajji A Abuja Afrika
AIG Kwaimo Ya Kai Ziyarar Aiki Gombe, Ya Buƙaci Ƙara Ƙaimi A Yaƙi Da Ta’addanci Labarai
Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal Ya Bar PDP Ya Koma APC Labarai
Kasashen Turai: Bazamu Yarda Da Dokar Harajin Trump Ba Labarai
Akwai Yiwuwar Iran Da Amurka Su Cimma Matsayar Dakatar Da Shirin Nukiliya Amurka
Jami’an Tsaro Sun Dakile Safarar Makamai Daga Jos Zuwa Jihar Neja Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Kasar Koriya Ta Arewa Ya Zamo Sakataren Jam’iya Mai Mulki Labarai
  • Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe Afrika
  • Hukumar Zabe A Najeriya Ta Cigaba Da Rijistar Katin Zabe Labarai
  • Kotun Amurka Tana Tuhumar Wani Dan Jarida Amurka
  • NSC Ta Bai Wa Shugabannin NFF Sa’o’i 24 Su Yi Murabus Wasanni
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara Afrika
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.