Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Mayakan ISWAP Sun Kai Farmaki Kan Sojojin Najeriya
Published: January 30, 2026 at 5:36 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 30, 2026

Mayakan ISWAP da jiragen yaki marasa matuka wato drones suka rufawa baya, sun kai hari kan wani sansanin sojoji a jihar Barno,suka kashe sojoji masu yawa da asubahin ranar Alhamis, wannan yana kunshe ne cikin bayani da sojojin kasar suka bayar. Kuma wannan shine hari na biyu da mayakan suka kai wa dakarun kasar a yankin cikin makon nan.

Jiragen drones da mayakan ISWAP suke amfani da su a hare haren da suke kaiwa a baya bayan nan ya zafafa tarzoma a yankin, kamar yadda kakakin rundunar sojin Najeriya Leftanar kanar Sani Uba ya fada.

Mayakan na ISWAP sun afkawa sansanin dake Sabon Gari cikin dare sosai, suka kutsa cikin sansanin na wani dan gajeren lokaci, yayin da kuma ake gwabza fada, jiragen yakin su na drones, suka lalata motocin aikin sojojin, manya da kanana.

Wasu majiyoyi biyu ta fuskar tsaro sunce an kashe akalla sojoji 9, da ‘yan banga biyu, wasu 16 kuma suka jikkata.

A bana dai sojojin Najeriya sun kutsa sosai cikin yankin da mayakan sakan suke, a wani sabon yunkuri na kai musu farmaki a inda suke.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Matsalolin Masarautun Kano Sun Kawo Karshe
Next Post: Gwamnatin Sojan Burkina Faso Ta Soke Jam’iyyun Siyasar Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya Labarai
Gwamnatin Gombe Ta Raba Naira Miliyan 14 Ga Iyalen ‘Yan Jaridan Da Suka Rasu Najeriya
Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Masu Tayar Da Hankali Najeriya
Sunayen Jakadu: Kungiyar CISLAC Ta Nemi A Janye Sunan Mr. Ayodele Oke Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Mun Kwato Kimanin Naira Biliyan 40 Na Badakala A Tsawon Shekara Daya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran Amurka
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Mutane 70 A Nairobi Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Trump Yace Babu Maganar Kawo Karshen Yakin Amurka Da Iran Amurka
  • Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal Afrika
  • Hawan Sallah Daga Masarautar Misau Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.