Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya Afrika
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad Afrika
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida Afrika
  • Zargin Fitar Da Bayanan Masu Zabe A Najeriya Afrika
  • NAHCON Ta Fara Shirye-shiryen Dawowar Alhazai Afrika

Gwamnatin Najeriya Zata Rabawa Al’umma Tallafin Noma
Published: April 18, 2026 at 4:13 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana aniyar ta na ganin cewa tallafin dala miliyan 500 da Bankin Duniya ya amince da shi, ya isa hannun manoma na hakika a fadin kasar nan, maimakon karkata shi ga akwakun ‘yan siyasa.

Shugaban Hukumar Ba da Tallafin Kuɗaɗen Haɗin Gwiwa na Ƙasa (NFC), Emmanuel Atama, shi ne ya tabbatar da hakan yayin wata hira da aka yi da shi kwanan nan. Atama ya bayyana cewa shirin an tsara shi ne don ya amfani akalla manoma miliyan daya, tare da magance matsalolin da suka dabaibayi shirye-shiryen da suka gabata.

Atama ya bayyana cewa daya daga cikin manyan matsalolin da suka hana tallafin noma tasiri a baya shi ne tsoma bakin siyasa da kuma rashin sahihan bayanai.

“Yawancin shirye-shiryen da aka yi a baya sun fuskanci cikas sakamakon rashin isasshen bayani ga manoma da kuma tsoma bakin yan siyasa, wanda hakan ya hana kuɗaɗen isa ga waɗanda aka yi niyya,” in ji shi.

Ya kara da cewa wannan karon tsarin zai bambanta, musamman sakamakon hadin gwiwa da Ministan Noma mai kwazo, wanda ya nuna shirye-shiryen cire duk wata sarkakiya da ke kawo cikas wajen aiwatar da ayyukan hukumar.

Shugaban ya kuma bayyana cewa tattaunawar da suka yi da Bankin Duniya ta bankado kurakuran da aka tafi da su a shirye-shirye irin su Anchor Borrowers Program. Saboda haka, wannan sabon tsarin zai mayar da hankali ne wajen gyara wadannan kura-kurai.

A halin yanzu, hukumar ta riga ta fara zagaye domin wayar da kan manoma a jihohi daban-daban, inda ake karfafa musu gwiwa su shiga kungiyoyin hadin gwiwa (cooperatives).

Wannan shi ne zai ba da damar tantance su cikin sauki da kuma tabbatar da gaskiya wajen rabon tallafin.

Wani sabon salo da shirin zai zo da shi don toshe kofofin almundahana shi ne raba kayan aikin noma maimakon kudi tsantsa. Atama ya fayyace cewa, Za a fi mayar da hankali wajen samar da takin zamani, iri, da injinan noma. Idan har akwai buƙatar bayar da kudi kai tsaye, ba zai wuce kashi 10% zuwa 15% na jimillar tallafin da manomin zai samu ba.

Wannan matakin na zuwa ne a daidai lokacin da kasar ke fuskantar kalubalen hauhawar farashin abinci, inda ake fatan wannan tallafi zai bunkasa samar da abinci a fadin Najeriya.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz
Next Post: Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa

Karin Labarai Masu Alaka

Mutane Da Dama Sun Rasa Rayukansu Yayin Rikici A Uganda Siyasa
Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
Farashin Danyen Mai Ya Fadi A Kasuwar Duniya Afrika
Magajin Garin Istanbul Dake Kurkuku Ya Bukaci A Gudanar Da Zabe Labarai
Kasar Gambiya Ta Gayawa Kotun MDD Shirin Myanmar Akan Musulmai Afrika
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • JEI Da Abokan Hulɗar Sun Gudanar Da Aikin Shuka Itatuwa Domin Bikin Ranar Muhalli Ta Duniya
  • Mourinho Ya ƙara Ta’azzara Takaddamarsa Da Hukumomin ƙwallon ƙafar Turkiyya
  • Za’ayi Jana’izar Marigayi Ali Khamenei a Tehran, Qom da Mashhad
  • Lewandowski: Zan Kokarta Zura Kwallo Ta 90 Don Kafa Tarihi A Poland
  • An Fara Dawo Da Alhazain Najeriya Gida

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar China Ta Sauka Daga Ragamar Bada Bashi Labarai
  • Shugaban Kasar Amurka Yakara Hana Wasu Kasashe Shiga Amurka Ciki Harda Nijar Amurka
  • Nan Gaba Kadan Kwallon Badminton Zata Samu Karbuwa Kamar Kwallon Kafa A Duniya Labarai
  • Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
  • Shugaban Rasha Yafara Ganawa Da Jakadun Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Ukraine Amurka
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami Afrika
  • Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
  • Isra’ila Ta Kai Hari Cibiyar Makamashin Nukiliyar Iran Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.