Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Najeriya Zata Rabawa Al’umma Tallafin Noma
Published: April 18, 2026 at 4:13 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana aniyar ta na ganin cewa tallafin dala miliyan 500 da Bankin Duniya ya amince da shi, ya isa hannun manoma na hakika a fadin kasar nan, maimakon karkata shi ga akwakun ‘yan siyasa.

Shugaban Hukumar Ba da Tallafin Kuɗaɗen Haɗin Gwiwa na Ƙasa (NFC), Emmanuel Atama, shi ne ya tabbatar da hakan yayin wata hira da aka yi da shi kwanan nan. Atama ya bayyana cewa shirin an tsara shi ne don ya amfani akalla manoma miliyan daya, tare da magance matsalolin da suka dabaibayi shirye-shiryen da suka gabata.

Atama ya bayyana cewa daya daga cikin manyan matsalolin da suka hana tallafin noma tasiri a baya shi ne tsoma bakin siyasa da kuma rashin sahihan bayanai.

“Yawancin shirye-shiryen da aka yi a baya sun fuskanci cikas sakamakon rashin isasshen bayani ga manoma da kuma tsoma bakin yan siyasa, wanda hakan ya hana kuɗaɗen isa ga waɗanda aka yi niyya,” in ji shi.

Ya kara da cewa wannan karon tsarin zai bambanta, musamman sakamakon hadin gwiwa da Ministan Noma mai kwazo, wanda ya nuna shirye-shiryen cire duk wata sarkakiya da ke kawo cikas wajen aiwatar da ayyukan hukumar.

Shugaban ya kuma bayyana cewa tattaunawar da suka yi da Bankin Duniya ta bankado kurakuran da aka tafi da su a shirye-shirye irin su Anchor Borrowers Program. Saboda haka, wannan sabon tsarin zai mayar da hankali ne wajen gyara wadannan kura-kurai.

A halin yanzu, hukumar ta riga ta fara zagaye domin wayar da kan manoma a jihohi daban-daban, inda ake karfafa musu gwiwa su shiga kungiyoyin hadin gwiwa (cooperatives).

Wannan shi ne zai ba da damar tantance su cikin sauki da kuma tabbatar da gaskiya wajen rabon tallafin.

Wani sabon salo da shirin zai zo da shi don toshe kofofin almundahana shi ne raba kayan aikin noma maimakon kudi tsantsa. Atama ya fayyace cewa, Za a fi mayar da hankali wajen samar da takin zamani, iri, da injinan noma. Idan har akwai buƙatar bayar da kudi kai tsaye, ba zai wuce kashi 10% zuwa 15% na jimillar tallafin da manomin zai samu ba.

Wannan matakin na zuwa ne a daidai lokacin da kasar ke fuskantar kalubalen hauhawar farashin abinci, inda ake fatan wannan tallafi zai bunkasa samar da abinci a fadin Najeriya.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu: Sojojin Mu Sun Yi Rawar Gani Don Kare Demokuraɗiyya A Jamhuriyar Binin Labarai
Rikicin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Man Fetur A Najeriya Afrika
Sanyin Hunturu Yayi Ajalin ‘Yan Cirani A Morocco Afrika
Hukumar Hasashen Kasuwanci Na Zargin Saida Bayanan Sirri Amurka
FRSC Gombe: Hatsarin Mota Ya Yayi Ajalin Mutane 38 Ya Jikkata Fiye Da 218 A Wata Ɗaya Najeriya
An Gargadi Kasar Canada Game Da Tura Sojoji Lebanon Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Najeriya Zata Rabawa Al’umma Tallafin Noma
  • Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz
  • Shugaba Tinubu Yasa Hannu Kan Dokar Kasafin 2026
  • Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11 Najeriya
  • Baitul Malin Amurka Zata Bawa Venezuela Da Cuba Damar Sayar Da Mai Amurka
  • Hukumar NDLEA Ta Kama Miyagun Kwayoyi A Edo Afrika
  • Amurka Ta Daina Bawa Israila Bayanan Sirri Amurka
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Anakan Bincike Wajen Gano Dan Bindigar Da Ya Kashe Dalibai Biyu A Jihar Rhode Island Amurka
  • Dakarun Gwamnatin Kasar Sham Tayi Mamaya Zuwa Gabashin Kasar Labarai
  • Jirgin Sama Ya Fadi A Kano Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.