Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina
Published: January 28, 2026 at 7:48 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan sanda 3 sun rasa rayukan su, yayin da wasu 2 suka jikkata lokacin da ‘yan ta’adda dauke da makamai suka kai hari kan ‘yan sanda masu sintiri a jihar Katsinan Najeriya ranar Talata, a cewar ‘yan sanda ranar laraba.

Wannan na daga cikin karuwar hare-hare da ‘yan ta’adda ke kaiwa, da ya hada da garkuwa da mutane da ‘yan bindiga ke yi idan sun far wa makarantun da wuraren ibada, a arewa maso yammacin kasar.

Mai magana da yawun ‘yan sandan jihar Katsina, Abubakar Sadiq Aliyu ya ce an far ma ‘yan sandan ne a wajen hanyar Guga da Bakori lokacin da suke sintiri. Ya ce ‘yan sandan sun nuna jarumta sosai wajen mai da wuta, inda suka fattattaki ‘yan ta’addan, amma sun rasa jami’ai uku a musayar wuta. ‘Yan sanda biyu da suka samu raunuka na karbar magani a wani asibiti da ke kusa da inda abun ya faru.

A wani labarin kuma, a dai Najeria, a yau ‘yan sanda a jihar Lagos sun harbawa masu zanga-zanga kan rushe sansanin gidajen talakawa dake gab da teku da gwamnatin jihar ta yi tear gas, inda daya daga cikin masu zanga-zangar ya samu rauni. Rushe gine-ginen ya jawo da dubbannan mutane rasa matsugunin su.

Jami’ai a jihar Lagos, tare da taimakon ‘yan sanda da mashunan tonon kasa, sun fara rushe gidajen talakawa a unguwar Makoko, inda suka ce mazauna wurin sun gina gidajen nasu ne ba bisa ka’ida ba, wadanda yawanci gidajen katako ne aka gina su a saman ruwa, kusa da injunan lantarki masu hatsari.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kotu A Kasar Uganda Ta Bada Belin ‘Yar Gwagwarmaya
Next Post: Maganganun Jami’an Shige Da Fice Dana Shugaban Kasa Trump Suna Cin Karo Da Juna

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika
Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
Maharan Bindiga Sun Kashe Mutane 12 Masu Hakar Ma’adanai A Jihar Filato Labarai
Shugabannin Kiristoci Sun Halarci Filin Idi A Kaduna Domin Nuna Haɗin Kai Afrika
Man Da Matatar Dangote Take Fitarwa Zuwa Kasashen Afirka Ya Karu Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai
  • Gwamnan Jihar Filato Na Shirin Komawa APC Siyasa
  • ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayin Shanu Tsaro
  • Fadar Shugaban Kasa Ta Karyata Jita-Jitar Yunkurin Sanya Wa Tinubu Guba A Abinci Afrika
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno Afrika
  • Kasashen Mali Da Burkina Faso Sun Haramtawa Amurkawa Shiga Kasashen Afrika
  • Liverpool Tayi Rashin Nasara A Wasanni Tara Wasanni
  • Ana Cigaba Da Ceto Masunta Daga Ruwa A Ghana Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.