Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina
Published: January 28, 2026 at 7:48 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan sanda 3 sun rasa rayukan su, yayin da wasu 2 suka jikkata lokacin da ‘yan ta’adda dauke da makamai suka kai hari kan ‘yan sanda masu sintiri a jihar Katsinan Najeriya ranar Talata, a cewar ‘yan sanda ranar laraba.

Wannan na daga cikin karuwar hare-hare da ‘yan ta’adda ke kaiwa, da ya hada da garkuwa da mutane da ‘yan bindiga ke yi idan sun far wa makarantun da wuraren ibada, a arewa maso yammacin kasar.

Mai magana da yawun ‘yan sandan jihar Katsina, Abubakar Sadiq Aliyu ya ce an far ma ‘yan sandan ne a wajen hanyar Guga da Bakori lokacin da suke sintiri. Ya ce ‘yan sandan sun nuna jarumta sosai wajen mai da wuta, inda suka fattattaki ‘yan ta’addan, amma sun rasa jami’ai uku a musayar wuta. ‘Yan sanda biyu da suka samu raunuka na karbar magani a wani asibiti da ke kusa da inda abun ya faru.

A wani labarin kuma, a dai Najeria, a yau ‘yan sanda a jihar Lagos sun harbawa masu zanga-zanga kan rushe sansanin gidajen talakawa dake gab da teku da gwamnatin jihar ta yi tear gas, inda daya daga cikin masu zanga-zangar ya samu rauni. Rushe gine-ginen ya jawo da dubbannan mutane rasa matsugunin su.

Jami’ai a jihar Lagos, tare da taimakon ‘yan sanda da mashunan tonon kasa, sun fara rushe gidajen talakawa a unguwar Makoko, inda suka ce mazauna wurin sun gina gidajen nasu ne ba bisa ka’ida ba, wadanda yawanci gidajen katako ne aka gina su a saman ruwa, kusa da injunan lantarki masu hatsari.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kotu A Kasar Uganda Ta Bada Belin ‘Yar Gwagwarmaya
Next Post: Maganganun Jami’an Shige Da Fice Dana Shugaban Kasa Trump Suna Cin Karo Da Juna

Karin Labarai Masu Alaka

Koriya Ta Arewa Ta Gudanar Da Gwajin Makami Mai Linzami Tsaro
EFCC Ta Cafke Fitacciyar Jarumar Kannywood Samha Inuwa Labarai
Bola Ahmed Tinubu Ya Soke Bashin Da Gwamnati Take Bin NNPC Najeriya
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutane A Kauyuka Dake Yammacin A Najeriya Najeriya
An Samu Nasarar Karbo Karin Yara 130 Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Wani Jirgi Yayi Saukar Angulu Ba Shiri Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Mata Manoma A Najeriya Ta Raba Kyautar Abinci A Gombe
  • Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi
  • ‘Yan Sandan Najeriya Sunyi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda A Katsina
  • Iran Ta Tsagaita Kai Hare Hare Makwabta
  • Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Mayakan ISWAP Sun Kai Farmaki Kan Sojojin Najeriya Najeriya
  • Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
  • Wani Ya Yiwa ‘Yar Sa Mai Shekaru 8 Fyade A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Umar Ya Lashe Kyautar Gwarzon ‘Dan-Wasa Na 2025 Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto Labarai
  • Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot. Wasanni
  • Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Ta Bukaci Rwanda Ta Daina Marawa ‘Yan Tawayen M23 Baya Afrika
  • Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.