Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri 
Published: March 18, 2026 at 1:52 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: March 18, 2026

Shugabannin Sojojin Najeriya sun Kai Ziyarar Aiki Maiduguri

Daga Adamu Aliyu Ngulde, Maiduguri

Babban Hafsan Tsaron Najeriya Janar O.O Oluyede, da Babban Hafsan Rundunar Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, sun isa birnin Maiduguri na Jihar Borno domin shaida yanayin da ake ciki na matsalar tsaro da kuma jajantawa al’ummar jihar Borno.

Ziyarar tasu na zuwa ne ƙasa da sa’o’i 24 da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayar na tura dukkan hafsoshin tsaro zuwa Maiduguri, sakamakon jerin hare-haren ƴan ta’adda, ciki har da fashewar bama-bamai guda uku a yammacin ranar Litinin, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar sama da mutane 20 tare da jikkata fiye da 100.

Shugabannin sojojin sun sauƙa a sansanin sojin sama da ke Maiduguri, inda kwamandan rundunar haɗin gwiwa ta yankin Arewa maso Gabas (Operation Hadin Kai), da sauran manyan hafsoshin soji suka karɓe su.

Ziyarar na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na magance ƙaruwar hare-haren ƴan ta’adda a jihar Borno, musamman bayan hare-haren bama-bamai na baya-bayan nan da ake zargin mayakan Boko Haram/ISWAP ne suka kai.

Tun da farko dai, Shugaba Tinubu ya yi Allah-wadai da hare-haren, inda ya bayyana su a matsayin “ayyukan mugunta na ƙungiyoyin ta’addanci masu muguwar aniya,” tare da alƙawarin ƙara ƙaimi wajen yaƙar dukkan ƙungiyoyin ƴan ta’adda.

A halin yanzu, rundunar soji na ci gaba da ƙoƙarin dawo da zaman lafiya da tsaro mai inganci a yankunan da abin ya shafa, ta hanyar ƙara sa ido da kuma ƙarfafa matakan tsaro.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Bayyana ‘Yan Bindiga Da Cewa Ruwa Yakarewa Dan Kada
Next Post: Kasar Saudiya Zata Cika Azumi Talatin

Karin Labarai Masu Alaka

Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC Labarai
SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne Labarai
Hawan Durba A Fadar Sarkin Zazzau Afrika
Shugaba Tinubu Ya Taya Musulmai Murnar Sallah, Tare Da Kira Zuwa Ga Kishin Kasa Afrika
Gwamnatin Gombe Ta Raba Naira Miliyan 14 Ga Iyalen ‘Yan Jaridan Da Suka Rasu Najeriya
Kasar Afirka Ta Kudu Ta Gayyaci Sabon Jakadan Amurka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Dillalan Mai Suna Fuskantar Karancin Mai Sakamakon Yakin Amurka Da Iran Afrika
  • Jami’ai A Mexico Sun Tabbatar Da Kashe Shugaban Masu Shan Ƙwaya Nemesio Oseguera Labarai
  • Magoya Bayan Dan Hamayya A Afirka Ta Kudu Sun Hallara A Kotu Afrika
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza Labarai
  • ‘Yan Sanda A Tsibirin Bahamas Sun kama Mijin Wata Ba Amurkiya Amurka
  • Shugaba Trump Yace Amurka Zata Janye Yaki Da Iran Afrika
  • Farashin Mai Ya Tashi A Kasuwannin Duniya Labarai
  • Sojoji Sun Dakile Harin ’Yan Ta’adda a Kukareta Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.