Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Meyasa Israela Take Hana Kaiwa Gaza Kayan Tallafi
Published: February 6, 2026 at 11:03 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan gwagwarmaya da suka shirya jerin gwanon jiragen ruwa dauke da tallafin abinci da magunguna zuwa Gaza a bara, wadanda Isra’ila ta hana su kai tallafin suna shirin za su sake gwada daukar matakin a bana ma. Suna sa ran jiragen ruwan da zasu shiga tattakin su ninka na bara dauke da ma’aikatan kiwon lafiya fiye da dubu daya.

A bara Isra’ila ta dakatar jerin gwanon jiragen ruwan da suka kai 40 cikin watan oktoban bara, suka kama ‘yar gagwarmayan nan daga Sweeden Greta Thunberg da wasu mutane 450.

‘Yan Gwagwarmaya da suka hallara a harabar gidauniyar marigayi tsohon shugaban Afirka ta Kudu Nelson Mandela a ranar laraba a birnin Johanesburg, sunce jiragen ruwa 100 ne suke sa ran za su shiga tafiyar ta bana.

Jami’an Isra’ila sun sha yin tur da Allah wadai da matakan na ‘yan gwagwarmaya, suna masu cewa wannan ba komi bane, illa halin dan zakara mai neman suna.

Isra’ila wacce take da iko kan dukkanin hanyoyin shiga Gaza, ta musanta cewa tana hana Shigar da kayan agaji da sauransu kai wa ga Falasdinawa fiye da su milyan 2 a Gaza. Kungiyoyin agaji na Falasdinu da kuma saura daga kasashen duniya duk sunce kayayyaki da suke isa Gaza sun gaza, duk da yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma a cikin watan oktoban bara wadda a ciki aka bada tabbacin kara yawan kayayyakin masarufi da sauran su zuwa yankin.

Afrika, Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kasar Morocco Ta Kwashe ‘Yan Kasar Daga Sassan Ambaliyar Ruwa
Next Post: China Ta Kori Wakilan Majalisar Dokoki Uku A Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Donald Trump Ya Bayyana Cewa Yana Cikin Masu Zaben Sabon Jagoran Iran Amurka
Gwamnatin Kebbi Ta Samu Tankokin Yaki Tsaro
An Kai Hari Babbar Tashar Iskar Gas A Iran Afrika
Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal Afrika
Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela Amurka
Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Taki Da Mai Ga Manoma Labarai
  • Tsohuwar Ministan Albarkatun Mai Ta Bayyana A Kotu Najeriya
  • Togo Ta Kama Tsohon Shugaban Kasar Burkina Faso Saboda Kitsa Juyin Mulki Afrika
  • Jam’iyyar APC Ta Rantsar Da Sabbin Shugabanni a Jihar Neja Labarai
  • Kamfanin Dangote Zai Sayo Na’urori Daga Kasar China Kimiya
  • CP Chuso Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Gwiwar Hukumomin Tsaro A Gombe Afrika
  • Amurka Tafara Mayar Da ‘Yan Afghanistan Da Suka Makale A Qatar Amurka
  • CAF Ta Yanke Hukunci Kan Ƙasashen Senegal Da Moroko AFCON 2025 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.