Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Togo Ta Kama Tsohon Shugaban Kasar Burkina Faso Saboda Kitsa Juyin Mulki
Published: January 20, 2026 at 8:09 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Togo ta kama tsohon shugaban kasar Burkina Faso, kuma ta tusa keyarsa zuwa kasar sa, bayan da jami’ai a Ouagadougou suka yi zargin yana kitsa juyin mulki, kamar yada wasu majiyoyi biyu suka fadawa kamfanin dillancin labarai na Reuters ranar talata.

Paul Henri Damiba, ya hau mulki ne a shekara ta 2022 sakamakon juyin mulki da sojoji suka yiwa gwamnatin farar hular kasar, wacce tayi bakin jini saboda yadda ‘yan tawaye masu ikirarin Islama suke tada kayar baya.

Sai dai shi ma Damiba, da ya kasa shawo kan fitinar ‘yan bindigar, lamarin ya harzuka dakarun kasar dake yammacin Afirka, shi ma aka yi masa juyin mulki a cikin shekarar da ya hau mulki, mataki da ya kawo shugabancin Ibrahim Traore, wanda yake ci gaba da mulkin kasar.

A farkon wannan wata, Burkina Faso tace ta wargaza wan yunkurin kashe Troare, da take zargin Damiba da kullawa, wanda yake zaman gudun hijra a Lome babban birnin kasar Togo.

Wata majiya ta fuskar tsaro, da wata majiya kusa da fadar shugaban kasar Togo, sun gayawa Reuters a ranar talata cewa, an kama Damiba, ranar Asabar, kuma an maida shi Burkina Faso.

A dai ranar Talatan gwamnatin kasar Togo ta tabbatar da wannan labari, kuma cikin sanarwar da ta bayar wacce aka rubuta ranar Litinin, sannan aka raba, Damiba, yana fuskantar zargin almubazzaranci da dukiyar al’umma, arzurta kansa ba bisa ka’ida ba, rashawa da kuma halatta kudaden haram, amma sanarwa bata ambaci zargin juyin mulki ba.

Kamfanin dillancn labarai na Reuters, ya kasa magana da Damiba, kuma babu tabbas ko yana da lauya a Togo. Gwamnatin Burkina Faso, bata maida martani ba da aka nemi jin ta bakinta.

Afrika, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Tsohon Shugaban Kasa Obasanjo Ya Ziyarci IBB
Next Post: Sojojin Kasar Uganda Sun Bazama Neman Bobi Wine Sakamakon Rikicin Bayan Zabe

Karin Labarai Masu Alaka

Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya Afrika
Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
Amurka Ta Girke Jirage Marasa Matuki Tare Da Sojoji A Najeriya Afrika
Kasar Netherland Ta Mayarwa Masar Mutum Mutumin Tarihi Afrika
Amurka Ta Jefa Makamin Tomahawk A Makarantar Yara Mata Afrika
PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mala Buni: Zai Jagoranci Kwamitin Sassanci Na Jam’iyar APC Labarai
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NYSC – Sai An Gabatar Da Takardar NERD Kafin Shiga Bautar Ƙasa Afrika
  • Pakistan Zata Karbi Tattaunawar Rikicin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi Afrika
  • Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
  • Za’a Ninka Shekarun Kurkuku Ga Masu Aikata Luwadi A Senegal Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.