Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Kotun Tarayya Ta Yankewa Nnamdi Kanu Daurin Rai-da-Rai
Published: November 20, 2025 at 5:25 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 21, 2025

Wata kotu a Najeriya ta yanke hukumcin daurin rai da rai a gidan kurkuku, a kan madugun kungiyar ‘yan awaren nan ta Biafra, ta kudu maso gabashin Najeriya, Nnamdi Kanu, bayan da ta same shi da dukkan laifuffuka guda 7 da aka tuhume shi da aikatawa da suka shafi ta’addanci.

Mai shari’a Ja’es Omotosho na babbar kotun tarayya dake Abuja, yace masu gabatar da kararraki sun tabbatarwa kotun cewa irin kalamun da yayi da aka watsa ta kafar rediyo da kuma umurnin da yayi ta ba magoya bayan kungiyarsa ta “Indigenous People of Biafra” ko IPOB a takaice, sun haddasa kai munanan hare-hare da suka janyo hasarar rayukan jami’an tsaro da fararen hula.

Wannan zub da jinin wani bangare ne na yunkurin da yake jagoranta na kawowa ga ballewar yankin da mafi yawan al’ummarta ‘yan kabilar Igbo ne. A shekarar 1967, yankin yayi yunkurin ballewa ta hanyar ayyana Jamhuriyar Biafra, abinda ya haddasa yakin basasar shekaru uku, inda mutane fiye da miliyan daya suka mutu.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Jihar Kano Zata Kashe Makudan Kudade Ga Jama’ar Kano!
Next Post: Shirin Dare 2030 UTC Yau Alhamis 11.20.2025

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika
Kotu Tayi Watsi Da Tarukan ADC Bangaren David Mark Afrika
Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kasar Saudiya Ta Sanar Da Ganin Watan Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayin Shanu Tsaro
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
  • Tsohon Jagoran Masu Kishin Kasa A Hungry Ya Amince Da Shan Kaye Labarai
  • Tsohon Gwamnan Jihar Kano Rabi’u Musa Kwankwaso Ya Fice Daga NNPP Afrika
  • Gwamnatin Trump Tana Cigaba Da Korar Baki Daga Amurka Afrika
  • Mawakiyar Amurka Cardi B. Ta Cashe A Saudi Araibiya Nishadi
  • Jami’an Shige Da Ficen Amurka Sun Harbe Wani Har Lahira Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.