Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Amurka Tafara Mayar Da ‘Yan Afghanistan Da Suka Makale A Qatar
Published: February 12, 2026 at 7:58 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fara biyan ‘yan kasar Afghanistan da suka makale a Qatar kudi domin su koma kasar su, a wani yunkur na rufe sansanin da suke zaune, bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya dakatar da shirin sake tsugunar da su a Amurka, domin fargabar da suke yi cewa zaman su a Afghanistan za su fuskanci damuwa da gwamnatin kasar domin alakar su da Amurka, kamar yadda wani babban jami’in ma’aikatar ya gayawa wakilan majalisar dokokin Amurk a ranar laraba.

Fiye da ‘yan kasar Afganistan dubu daya da dari daya ne suke zaune a wani sansanin sojojin Amurka tun farkon shekarar da ta wuce, wadanda masu raji suka ce sun hada da farar hula, da wadanda suka yi ayyuka na musamman da dakarun Amurka, a tsawon shekatu 20 da tayi tana yaki a kasar, wasu daga cikin su iyalan sojojin Amurka ne, wadanda dukkan su za su fuskanci mahadin gaske idan suka koma Afghanistan.

Wakilan majalisar ‘yan democrat sunyi Allah wadai da shirn gwamnatin Trump na biyan ‘yan Afghanistan din, wadanda suk yarda za su koma kasar su, gabannin shirin Amurka na rufe sansanin da suke ciki a cikin watan Maris mai zuwa.

Mataimakin Sakataren harkokin wajen Amurka Paul Kapur yace yayi imani kamar mutum 150 sun karbi kudi kuma sun koma kasar su, sai dai bai san makomar su bayan da suka koma Afghanistan ba.

Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Donald Trump Yace Basu Cimma Matsaya Da Benjamin Natanyahu Ba
Next Post: Rasha Takai Mummunan Hari Birnin Kyiv

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci Afrika
Kasashen Daular Larabawa Tare Da Saudiya Da Jordan Sunyi Allah Wadai Da kasar Israel Afrika
Gwamnatin Afirka Ta Kudu Na Kokarin Kafa Wasu Dokoki A Kasar Labarai
Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Jamus Akan Sha’anin Tsaro Labarai
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya Tayi Kakkausar Lafazi Game Da Harin Maiduguri
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno
  • Lauyoyi Sun Gurfanar Da Wani A Kotu Bisa Fasa Korin Kiyashi A Kenya
  • Anfara Gangamin Kafa Dokoki Masu Tsanani Ga ‘Yan Luwadi A Senegal

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Senegal Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirka Afcon 2025. Wasanni
  • CAF Ta Dakatar Da Kocin Senegal Pape Thiaw Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Hukumar NAHCON Ya Ajeye Mukaminsa Labarai
  • Jami’ai A Mexico Sun Tabbatar Da Kashe Shugaban Masu Shan Ƙwaya Nemesio Oseguera Labarai
  • Amurka Zata Aika Jiragen Yaki Biyu Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko Labarai
  • Majalisar Kwararrun Iran Ta Sanar Da Sabon Shugaban Addini Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Da Haɗin Guiwar Gwamnatin Jihar Zamfara Suna Shirin Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Jihar Rumbun Hotuna
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.