Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Amurka Tafara Mayar Da ‘Yan Afghanistan Da Suka Makale A Qatar
Published: February 12, 2026 at 7:58 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta fara biyan ‘yan kasar Afghanistan da suka makale a Qatar kudi domin su koma kasar su, a wani yunkur na rufe sansanin da suke zaune, bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya dakatar da shirin sake tsugunar da su a Amurka, domin fargabar da suke yi cewa zaman su a Afghanistan za su fuskanci damuwa da gwamnatin kasar domin alakar su da Amurka, kamar yadda wani babban jami’in ma’aikatar ya gayawa wakilan majalisar dokokin Amurk a ranar laraba.

Fiye da ‘yan kasar Afganistan dubu daya da dari daya ne suke zaune a wani sansanin sojojin Amurka tun farkon shekarar da ta wuce, wadanda masu raji suka ce sun hada da farar hula, da wadanda suka yi ayyuka na musamman da dakarun Amurka, a tsawon shekatu 20 da tayi tana yaki a kasar, wasu daga cikin su iyalan sojojin Amurka ne, wadanda dukkan su za su fuskanci mahadin gaske idan suka koma Afghanistan.

Wakilan majalisar ‘yan democrat sunyi Allah wadai da shirn gwamnatin Trump na biyan ‘yan Afghanistan din, wadanda suk yarda za su koma kasar su, gabannin shirin Amurka na rufe sansanin da suke ciki a cikin watan Maris mai zuwa.

Mataimakin Sakataren harkokin wajen Amurka Paul Kapur yace yayi imani kamar mutum 150 sun karbi kudi kuma sun koma kasar su, sai dai bai san makomar su bayan da suka koma Afghanistan ba.

Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Donald Trump Yace Basu Cimma Matsaya Da Benjamin Natanyahu Ba
Next Post: Rasha Takai Mummunan Hari Birnin Kyiv

Karin Labarai Masu Alaka

Sabon Ma’aikacin Tsaro Ne Ya Kashe Amurkawa Amurka
Rundunar Operation Endurance Peace Ta Gano Wajen Kera Makamai A Jihar Filato Afrika
An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango Labarai
Shugaban Amurka Zai Sake Gine Gaza Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Karo Na Biyu Cikin Kwanaki 29 An Samu Gobara A Kasuwar Katako Labarai
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa Afrika
  • Netanyahu Yayi Gaggawar Amincewa Da Kasafin Kudin Kasar Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Na Shirin Yin Zamiya Don Biyan Bashi Labarai
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran Amurka
  • Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
  • Sakataren Gwamnatin Amurka Ya Bayyana Bawa Kungiyoyin Agaji Damar Kai Taimako Sudan Amurka
  • Dalibai Sun Koma Makarantu A Wasu Jihohin Najeriya Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.