Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

An Kai Hari Babbar Tashar Iskar Gas A Iran
Published: March 18, 2026 at 9:51 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

A ranar Larabar ne aka kai hari kan babbar tashar iskar gas ta Pars a kasar Iran, wannan shine karon farko na kai hari kan kayayyakin makamashin Iran a mashigin tekun Fasha tun fara yakin Amurka da Isra’ila, lamarin da ya sa Tehran ta gargadi makwabtanta cewa za a kai hari kan na’urorin makamashin nasu “a cikin sa’o’i masu zuwa”.

Tashar Pars dai itace tashar iska mallakar Iran da take mafi girman tashar gas a duniya, wanda Iran ta raba da Qatar da ke gabar tekun Gulf. Kamfanin dillancin labaran kasar Iran ya bayar da rahoton cewa, an kai harin tankunan gas da wasu sassan matatar mai, an kwashe ma’aikata zuwa wani wuri don basu kariya, sannan kuma ma’aikatan gaggawa na kokarin kashe gobara.

Kafofin yada labaran Isra’ila sun yi ta yada labarin cewa Isra’ila ce ta kai harin tare da amincewar Amurka. Sojojin Isra’ila ba su amsa bukatar jin ta bakinsu ba.

Qatar, kawayen Amurka dake dauke da sansanin sojin saman Amurka mafi girma a yankin, ta kira harin da Isra’ila ta kai ba tare da ambaton wani rawar da Amurka ta taka ba. Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta kira lamarin “mai hadari da rashin da’a” wanda ya jefa tsaron makamashin duniya cikin hadari.

Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun shaida wa Saudiyya da Hadaddiyar Daular Larabawa da Qatar da su kwashe inasu-inasu a wasu wuraren samar da makamashi.

Afrika, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sallah Sai Ranar Juma’a A Najeriya: Fadar Sarkin Musulmi
Next Post: ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Cin Karensu Babu Babbaka A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Don Neman Zaman Lafiya Labarai
Sudan Takai Hari Kasar Chadi Da Jirgi Marar Matuki Afrika
Kasashe Biyar Zasu Tura Sojoji Domin Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya A Gaza Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Dalibin Jami’a Ya Rasa Ransa A Birnin Dakar Yayin Zanga Zanga Afrika
Sabon Babin Tsaro A Najeriya: Gombe Ta Fito Da Tsarin Smart Security Na Farko Afrika
An Damke Wani Likita Da Ke Taimakawa ‘Yan-Ta’adda Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kurdawa Sun Gargadi ‘Yan Uwansu Game Da Alaka Da Amurka Wajen Yakar Iran Afrika
  • Sanata Goje Yayi Watsi Da Fidda ‘Yan Takarar APC A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Kebbi Ta Samu Tankokin Yaki Tsaro
  • Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
  • Dakarun Operation Fansan Yamma Sun Ceto Mutane 48 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Afrika
  • Ana Cigaba Da Yaki Tsakanin Amurka Da Isra’ila Da Kasar Iran Afrika
  • ECOWAS Da AU Sun Nuna Damuwa Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau Afrika
  • Abba Kabir: Zamu Samar da Jirage Marasa Matuka A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.