Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

An Kai Hari Babbar Tashar Iskar Gas A Iran
Published: March 18, 2026 at 9:51 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

A ranar Larabar ne aka kai hari kan babbar tashar iskar gas ta Pars a kasar Iran, wannan shine karon farko na kai hari kan kayayyakin makamashin Iran a mashigin tekun Fasha tun fara yakin Amurka da Isra’ila, lamarin da ya sa Tehran ta gargadi makwabtanta cewa za a kai hari kan na’urorin makamashin nasu “a cikin sa’o’i masu zuwa”.

Tashar Pars dai itace tashar iska mallakar Iran da take mafi girman tashar gas a duniya, wanda Iran ta raba da Qatar da ke gabar tekun Gulf. Kamfanin dillancin labaran kasar Iran ya bayar da rahoton cewa, an kai harin tankunan gas da wasu sassan matatar mai, an kwashe ma’aikata zuwa wani wuri don basu kariya, sannan kuma ma’aikatan gaggawa na kokarin kashe gobara.

Kafofin yada labaran Isra’ila sun yi ta yada labarin cewa Isra’ila ce ta kai harin tare da amincewar Amurka. Sojojin Isra’ila ba su amsa bukatar jin ta bakinsu ba.

Qatar, kawayen Amurka dake dauke da sansanin sojin saman Amurka mafi girma a yankin, ta kira harin da Isra’ila ta kai ba tare da ambaton wani rawar da Amurka ta taka ba. Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Qatar ta kira lamarin “mai hadari da rashin da’a” wanda ya jefa tsaron makamashin duniya cikin hadari.

Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun shaida wa Saudiyya da Hadaddiyar Daular Larabawa da Qatar da su kwashe inasu-inasu a wasu wuraren samar da makamashi.

Afrika, Labarai, Sauran Duniya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Sallah Sai Ranar Juma’a A Najeriya: Fadar Sarkin Musulmi
Next Post: ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Cin Karensu Babu Babbaka A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

An Bude Kamfanin Sarrafa Ma’adanai A Kasar Mozambique Labarai
Jami’an Shiga Da Fice A Afirka Ta Kudu Sun Tafka Badakalar Kudade Afrika
Isra’ila Ta Zantar Da Hukuncin Kisa Ga Masu Kai Hare Hare Labarai
Jami’an Diflomasiyyar Iran Dana Amurka Sun Tattauna A Kasar Oman Afrika
Guinea Bissau Ta Tsaida Gwaje-Gwajen Allurar Rigakafin Shawara A Kasar Labarai
Amurka Zata Kamallah Yaki Da Iran A Makonni Biyu Masu Zuwa Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Amurka Ya Ya Bukaci Iran Ta Mika Wuya Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Tana Saka Ido Akan Matsalolin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Nada Shugaban NAHCON Labarai
  • China Ta Yi Kira Da Kasashen Gabas Ta Tsakiya Su Hada Kai Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Na Kokarin Hana Demokraɗiyya A Najeriya Siyasa
  • Hukumar ‘Yan Sanda Ta Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato Afrika
  • An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Don Neman Zaman Lafiya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.