Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela
Published: January 5, 2026 at 5:26 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

A yayin da ake ci gaba da zaman kaka-ni-ka-yi a kasar Venezuela, shugabar wucin gadi Delcy Rodriguez, a yanzu ta maye gurbin babban abokin huldar siyasar ta, shugaba Nicolas Maduro, wanda sojojin Amurka suka kama a wani farmakin cikin dare da suka kai a kasar.

Tun shekarar 2018 Rodriguez take rike da kujerar mataimakiyar shugaba Maduro, tana mai kula da harkokin tattalin arzikin kasar da ya dogara kusan kacokan kan man fetur, tana jagiorancin hukumar leken asirin kasar, kuma ita ce magajiyar kujerar shugabanci.

Rodriguez tana daga cikin manyan jami’an gwamnatin shugaba Maduro wadanda a bisa dukkan alamu sune suke rike da madafun iko na Venezuela, duk da cewa shugaba Donald Trump na Amurka da jami’ansa sun ce zasu matsa ma gwamnatin ta lamba don ganin ta yi aiki da manufofinsu game da kasar mai arzikin man fetur.

A ranar asabar ne kotun kolin kasar ta umurce ta da ta karbi ragamar shugabancin kasar, inda kuma ta samu goyon bayan rundunar sojojin Venezuela.

A cikin jawabin da tayi ma kasar ta talebijin, Rodriguez ba ta nuna alamun cewa zata hada kai da shugaba Trump ba, tana mai bayyana gwamnatinsa a zaman ta ‘yan tsagera.

A yayin da manyan jami’an fararen hula da na soja suke kewaye da ita, Rodriguez ta ce shugaba guda daya kasar Venezuela take da shi, kuma shine shugaba Nicolas Maduro, ta ce abinda ake aikata ma kasar Venezuela, ta’asa ce wadda ta keta dokoki na kasa da kasa.

Rodriguez, lauya kuma ‘yar siyasa mai shekaru 56 da haihuwa, ta jima tana wakiltar akidar gurguzu da juyin juya halin da marigayi shugaba Hugo Chavez ya kafa a kasar.

A ranar asabar da safe, an yi mamaki da aka ji shugaba Trump yana cewa sakataren harkokin wajensa Marco Rubio yayi magana da Rodriguez, kuma ta yi godiya, sannan zata yi aiki da gwamnatin Amurka yayinda Rubio yace gwamnatin Amurka zata iya yin aiki tare da Rodriguez, ba kamar Maduro ba.

Ranar lahadi, lafazin shugaba Trump ya canja a yayin da Rodriguez da sauran jami’an gwamnatin Venezuela suka ci gaba da caccakar gwamnatin sa, tare da jaddada cewa sune suke rike da kasar ba Amurka ba.

A cikin wata hirar da yayi da jaridar The Atlantic, shugaba Trump yayi barazanar cewa idan har ba ta yi abinda ya kamata ba, to zata dandana kudarta ita ma, fiye ma da Maduro.

A ranar lahadin kuma Rubio yace ba ya daukar Rodriguez da gwamnatinta a matsayin halaltattu a saboda a cewarsa, kasar ba ta gudanar da zaben gaskiya ba.

A halin da ake ciki, sakataren harkokin wajen na Amurka Marco Rubio, yace Amurka ba zata dauki nauyin gudanar da harkokin mulkin yau da kullum na Venezuela ba, sai dai zata ci gaba da matsa lamba ta hanyar tabbatar da ci gaba da yin aiki da takunkumin mai da aka sanya ma kasar.

Wannan kuwa, babban juyi ne daga kalamen da shugaba Trump yayi kwana guda kafin nan inda yace Amurka ce zata rika gudanar da harkokin kasar ta Venezuela a bayan hambarar da Nicolas Maduro da kama shi.

Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa
Next Post: Koriya Ta Arewa Ta Gudanar Da Gwajin Makami Mai Linzami

Karin Labarai Masu Alaka

Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe Labarai
Amurka Ta Kai ‘Yan Cirani Kamaru Afrika
Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
Shugaba Trump Ya Janye Karbar Kudin Fito Daga Wasu Kasashen Turai Amurka
Isra’ila Ta Dau Alwashin Kawo Karshen Falasdi Labarai
Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni
  • An Kaiwa Sojojin Ghana Hari Da Makami Mai Linzami
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal
  • ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya Farfardo Bisa Samun Wasu Sauye Sauye Labarai
  • Shugaba Donald Trump Ya Bayyana Cewa Yana Cikin Masu Zaben Sabon Jagoran Iran Amurka
  • Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Kara Sace Mutane A Jihar Naija! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Yanayin Sanyi Yayi Kamari a Yankin Gaza Tsaro
  • Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya Amurka
  • Farashin Danyen Mai Ya Fadi A Kasuwar Duniya Afrika
  • Yanbindiga sun Kashe kimanin mutane 30 a yankin kayama ta Jihar kwaran Najeriya Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.