Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika

Gwamnatin Bauchi: Ta Kaddamar Da Kwamitin Ma’adanai
Published: December 3, 2025 at 11:15 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 4, 2025

Gwamnatin Jihar Bauchi dake tarayyar Najeriya ta kaddamar da Kwamitin Cibiyar Koyon Harkokin Ma’adinai ta Alkaleri, Jihar Bauchi (MIABAS).

A yayin bikin kaddamarwar, Kwamishinan Harkokin Habaka Ma’adinai, Hon. Mohammed Maiwada Bello, ya yabawa hangen nesa da jagorancin Gwamnan Bala Mohammed, yana cewa cibiyar babban ginshiki ce da za ta inganta bincike, horaswa da kuma ƙwarewa a fannin ma’adinai.

Kwamishinan ya bayyana cewa MIABAS za ta taimaka wajen horar da matasa da kwararru a fannoni daban-daban kamar tono ma’adinai, sarrafawa, ƙara darajar ma’adinai da kuma kula da muhalli.

Hakan zai karfafa gina ƙwararru ‘yan gida, samar da ayyukan yi, da kuma tallafawa matasa a dukkan harkar ma’adinai.

An dora wa sabuwar kwamitin—wanda ya kunshi masana daga manyan ma’aikatu da cibiyoyi—alhakin kammala cikakken tsari na kafa MIABAS cikin watanni uku.

Kwamishinan ya bukaci mambobin su yi aiki da gaskiya da jajircewa domin gina cibiyar koyarwa da kirkire-kirkire ta ma’adinai wacce za ta amfanar da jihar nan da kasa baki ɗaya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Za’a Dauko Messi Aro Zuwa Barcelona Deco
Next Post: CAF, Zata Ci Tarar Wasu Kasashe AFCON 2025

Karin Labarai Masu Alaka

Kasar Rasha Ta Zargi Ukraine Da Kai Hari Gidan Shugaban Rasha Amurka
Gwannatin Jihar Kebbi Ta Arawa Maniyyata Kuɗin Aikin Hajji 2026, Labarai
Gwamnatin Sokoto Tabada Umarnin Biyan Albashin Watan Fabrairu Labarai
Kasar Mauritius Zata Rage Amfani Da Makamashi Afrika
Yakin Iran Da Isra’ila Da Amurka Zai Shafi Kasashen Afirka – Masana Afrika
Jaura Ta Bayyana A Wasu Jihohin Amurka Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kauran Gwandu Zai Inganta Wutan Lantarki A Kebbi Siyasa
  • FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • Suvr Jahun: Ya Kamata Obasanjo Ya Bar Al’umar Ƙasa Su Fito Da Wadda Suke So 2027 Najeriya
  • Kotu A Birnin Tarayya Abuja Ta Bada Belin Tsohon Minista Abubakar Malami Najeriya
  • Gwamnatin Jihar Filato Ta Sauke Hakimin Mushere Afrika
  • Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma Afrika
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
  • Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.