Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi Afrika

An Kaddamar Da Jigilar Maniyyata Aikin Hajji A Abuja
Published: May 3, 2026 at 8:30 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya, Sanata Kashim Shettima, ya yi kira ga maniyyata aikin Hajjin shekarar 2026 da su kiyaye dabi’u na gari wadanda za su fito da martabar Nijeriya fili, sannan su kasance jakadu nagari ga kasarsu yayin gudanar da ibada a kasa mai tsarki.

Shettima ya bayyana maniyyata a matsayin wakilan Nijeriya a idon duniya, inda ya bukace su da su nuna kyakkyawar dabi’a ta hanyar bin dokoki da oda na kasar Saudiyya.

Mataimakin Shugaban Kasar ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi, yayin da yake kaddamar da jigilar maniyyata ta farko na shekarar 2026 a Filin Jirgin Sama na kasa da kasa na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja. Ya nanata cewa gwamnati ta jajirce wajen tabbatar da tsaro, tsari, da jin dadin dukkan mahajjata.

“Ku jakadun Nijeriya ne. Kuna dauke da hoton kasarmu da mutuncin al’ummarmu. Halayenku su nuna tarbiya, tawali’u, hakuri, da gaskiya,” in ji shi.

An fara jigilar ne da mahajjata kusan 500 daga Jihar Kogi zuwa kasar Saudiyya, yayin da jimillar maniyyata 50,000 ne ake sa ran za su gudanar da aikin Hajjin na bana daga Nijeriya.

Da yake jawabi a wurin taron, Shettima ya bayyana cewa aikin Hajji wata tabbatacciyar yarjejeniya ce tsakanin gwamnatin Nijeriya da ’yan kasa, inda ya ce ya zama wajibi kan gwamnati ta sauke nauyin kula da su, su kuma maniyyata su kare mutuncin kasar.

Ya kara da cewa: “Aikinmu ne mu tabbatar kowane maniyyaci ya yi wannan tafiya ba tare da wata wahala ko fargaba ba. Nasarar wannan aikin ba ta dogara ne kawai kan yawan jiragen da suka tashi ba, a’a, tana ga jin dadin mahajjatanmu da kuma kauce wa duk wata nakasu da za a iya kauce mata.”

A nasa jawabin, Gwamnan jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo, ya bayyana aikin Hajji a matsayin wata dama ta musamman da ke bukatar sadaukarwa ga Allah. Ya bukaci maniyyata da su ci gaba da addu’o’i ga Najeriya, musamman kan zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki.

Haka zalika, ya nemi a taya Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da Mataimakinsa Shettima da addu’a yayin da suke kokarin gyara kasar nan ta hanyar manufofinsu na “Sabunta Fata” (Renewed Hope).

Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazzai ta Kasa (NAHCON), Ismail Abba Yusuf, ya tabbatar wa masu ruwa da tsaki cewa hukumar tana nan kan bakarta na tabbatar da jin dadin ’yan Nijeriya. Ya bayyana cewa hukumar tana fuskantar garambawul karkashin gwamnatin Shugaba Tinubu don tabbatar da gaskiya da kuma sauya fasalin aikin Hajji a kasar.

Taron ya samu halartar Karamar Ministar Abuja, Dr. Mariya Mahmoud Bunkure, da wakilin Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, wadanda duka suka jaddada kudurin gwamnati na ganin an kwashe mahajjata lafiya an kuma dawo da su lafiya.

Afrika, Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Allah Ya Yiwa Shahararren Dan Jarida Saleh Shehu Ashaka Rasuwa
Next Post: Sanata Goje Yayi Watsi Da Fidda ‘Yan Takarar APC A Gombe

Karin Labarai Masu Alaka

Aisha Buhari Ta Bayyana Irin Kalubalen Da Ta Fiskanta Sakamakon Biyewa Jita-Jita Labarai
Jagoran Adawar Uganda Bobi Wine Ya Fice Daga Kasar Afrika
Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba. Afrika
Gwamnatin Tinubu Zata Samar Da Wutan Solar A Jami’ar ADUST Wudil Afrika
Sakataren Kungiyar NATO Yayi Magana Da Hukumomin Kasashe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe
  • Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe
  • Ana Cigaba Da Shirye-Shiryen Fara Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cire Sharadin Rubuta UTME Ga Masu Neman Shiga Kwalejojin Ilimi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Mayakan RSF Sun Zafafa Kai Hare Hare Da Jirgi Maras Matuki A Sudan Labarai
  • Gwamnatin Najeriya Zata Farfado Da Cibiyar Koyon Sana’oi Ta Dangote Afrika
  • Kasashen Mali Da Burkina Faso Sun Haramtawa Amurkawa Shiga Kasashen Afrika
  • Shugaban Kasar Afirka Ta Tsakiya Ya Roki Rasha Ta Taimakawa Kasar Afrika
  • An Kusa Kawo Karshen Matsalolin Tsaro A Jihar Filato Afrika
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan Afrika
  • An Canza Shugabannin Hukumar Hakar Ma’adanai A Congo Labarai
  • Kamfanin Magani Na Aspen Yayi Gagarumar Asara A Cinikayya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.