Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya, Sanata Kashim Shettima, ya yi kira ga maniyyata aikin Hajjin shekarar 2026 da su kiyaye dabi’u na gari wadanda za su fito da martabar Nijeriya fili, sannan su kasance jakadu nagari ga kasarsu yayin gudanar da ibada a kasa mai tsarki.
Shettima ya bayyana maniyyata a matsayin wakilan Nijeriya a idon duniya, inda ya bukace su da su nuna kyakkyawar dabi’a ta hanyar bin dokoki da oda na kasar Saudiyya.
Mataimakin Shugaban Kasar ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi, yayin da yake kaddamar da jigilar maniyyata ta farko na shekarar 2026 a Filin Jirgin Sama na kasa da kasa na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja. Ya nanata cewa gwamnati ta jajirce wajen tabbatar da tsaro, tsari, da jin dadin dukkan mahajjata.
“Ku jakadun Nijeriya ne. Kuna dauke da hoton kasarmu da mutuncin al’ummarmu. Halayenku su nuna tarbiya, tawali’u, hakuri, da gaskiya,” in ji shi.
An fara jigilar ne da mahajjata kusan 500 daga Jihar Kogi zuwa kasar Saudiyya, yayin da jimillar maniyyata 50,000 ne ake sa ran za su gudanar da aikin Hajjin na bana daga Nijeriya.
Da yake jawabi a wurin taron, Shettima ya bayyana cewa aikin Hajji wata tabbatacciyar yarjejeniya ce tsakanin gwamnatin Nijeriya da ’yan kasa, inda ya ce ya zama wajibi kan gwamnati ta sauke nauyin kula da su, su kuma maniyyata su kare mutuncin kasar.
Ya kara da cewa: “Aikinmu ne mu tabbatar kowane maniyyaci ya yi wannan tafiya ba tare da wata wahala ko fargaba ba. Nasarar wannan aikin ba ta dogara ne kawai kan yawan jiragen da suka tashi ba, a’a, tana ga jin dadin mahajjatanmu da kuma kauce wa duk wata nakasu da za a iya kauce mata.”
A nasa jawabin, Gwamnan jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo, ya bayyana aikin Hajji a matsayin wata dama ta musamman da ke bukatar sadaukarwa ga Allah. Ya bukaci maniyyata da su ci gaba da addu’o’i ga Najeriya, musamman kan zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki.
Haka zalika, ya nemi a taya Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da Mataimakinsa Shettima da addu’a yayin da suke kokarin gyara kasar nan ta hanyar manufofinsu na “Sabunta Fata” (Renewed Hope).
Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazzai ta Kasa (NAHCON), Ismail Abba Yusuf, ya tabbatar wa masu ruwa da tsaki cewa hukumar tana nan kan bakarta na tabbatar da jin dadin ’yan Nijeriya. Ya bayyana cewa hukumar tana fuskantar garambawul karkashin gwamnatin Shugaba Tinubu don tabbatar da gaskiya da kuma sauya fasalin aikin Hajji a kasar.
Taron ya samu halartar Karamar Ministar Abuja, Dr. Mariya Mahmoud Bunkure, da wakilin Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, wadanda duka suka jaddada kudurin gwamnati na ganin an kwashe mahajjata lafiya an kuma dawo da su lafiya.


