Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Sanata Sa’idu Alkali Ya Kaurace Wa Zaben Fidda Gwani
Published: May 20, 2026 at 8:50 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Sanata Sa’idu Ahmed Alkali ya sanar da kauracewa shiga zaɓen fidda gwani na gwamnan jihar Gombe ƙarƙashin jam’iyyar APC, wanda aka shirya gudanarwa ranar Alhamis 21 ga watan Mayun 2026.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Umar Alkali Jibrin ya fitar, Sanatan ya ce ya ɗauki matakin ne sakamakon abin da ya bayyana a matsayin rashin gaskiya da kuma take dokokin zaɓe a zaɓukan fidda gwani na kujerun Majalisar Wakilai da na Majalisar Dattawa da aka gudanar a wasu sassan jihar.

Sanarwar ta ce zaɓukan da aka gudanar a mazabun Gombe, Kwami da Funakaye da Billiri da Balanga, da kuma Yankin Sanatan Gombe ta Tsakiya, sun kasance cike da maguɗi, rashin bayyana gaskiya da kuma rashin bin ƙa’idojin da Dokar Zaɓe ta 2026 da kundin tsarin jam’iyyar APC suka tanada.

Sanata Alkali Wanda shine Tsohon Ministan Sufurin Najeriya, ya bayyana cewa an sanar da sakamakon wasu zaɓukan ba tare da gudanar da sahihin zaɓe ba, inda ya ce an gudanar da tsarin ba tare da kayan zaɓe, jami’an gudanarwa da masu sanya ido yadda ya kamata ba.

Ya ƙara da cewa waɗannan matsaloli sun sa jama’a da masu ruwa da tsaki suka rasa amincewa da tsarin zaɓukan fidda gwani a jihar.

Sai dai duk da kauracewar tasa, Sanata Alkali ya jaddada biyayyarsa ga jam’iyyar APC tare da bayyana aniyarsa ta ci gaba da mara wa jam’iyyar baya domin samun nasara a babban zaɓen shekarar 2027.

Haka kuma ya yi kira ga shugabannin APC na ƙasa da su soke zaɓukan da aka gudanar a yankunan da ake korafi a kansu, tare da kafa wani kwamiti na musamman domin gudanar da sahihin zaɓe cikin gaskiya da adalci.

Sanata Alkali ya kuma gode wa magoya bayansa da al’ummar jihar Gombe bisa haƙuri da natsuwar da suke nunawa duk da halin da ake ciki.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Zargin Tauye Ka’idojin Zabe: Malam Pantami Ya Janye Daga Takara
Next Post: Najeriya Da Poland Za Su Hada Kai Kan Tsaro da Bunƙasa Tattalin Arziki

Karin Labarai Masu Alaka

Dakarun Sojin Amurka Sunfara Sauka A Najeriya Amurka
Kasar Botswana Na Samun Kudaden Shiga Da Lu’ulu’u Labarai
Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
Tinubu Yafara Wasu Dabaru Domin Samun Kuri’u Siyasa
Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara Labarai
Manoma Suna Fuskantar Barazanar Karyewa A Kasar Ghana Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • NYSC – Sai An Gabatar Da Takardar NERD Kafin Shiga Bautar Ƙasa Afrika
  • Kasar Kenya Zata Samar Da Makamashi Labarai
  • An Hana Yada Rahotannin Siyasa A Kasar Uganda Tsaro
  • Anyi Rashin Mutane Da Yawa Yayinda Bom Ya Fashe Ana Sallar Magariba Maiduguri Labarai
  • Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
  • Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa Afrika
  • Rikicin Siyasa A Jihar Rivers Sakamakon Ayyana Fubara A Matsayin Shugaban APC Siyasa
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.