Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Sanata Sa’idu Alkali Ya Kaurace Wa Zaben Fidda Gwani
Published: May 20, 2026 at 8:50 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Sanata Sa’idu Ahmed Alkali ya sanar da kauracewa shiga zaɓen fidda gwani na gwamnan jihar Gombe ƙarƙashin jam’iyyar APC, wanda aka shirya gudanarwa ranar Alhamis 21 ga watan Mayun 2026.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Umar Alkali Jibrin ya fitar, Sanatan ya ce ya ɗauki matakin ne sakamakon abin da ya bayyana a matsayin rashin gaskiya da kuma take dokokin zaɓe a zaɓukan fidda gwani na kujerun Majalisar Wakilai da na Majalisar Dattawa da aka gudanar a wasu sassan jihar.

Sanarwar ta ce zaɓukan da aka gudanar a mazabun Gombe, Kwami da Funakaye da Billiri da Balanga, da kuma Yankin Sanatan Gombe ta Tsakiya, sun kasance cike da maguɗi, rashin bayyana gaskiya da kuma rashin bin ƙa’idojin da Dokar Zaɓe ta 2026 da kundin tsarin jam’iyyar APC suka tanada.

Sanata Alkali Wanda shine Tsohon Ministan Sufurin Najeriya, ya bayyana cewa an sanar da sakamakon wasu zaɓukan ba tare da gudanar da sahihin zaɓe ba, inda ya ce an gudanar da tsarin ba tare da kayan zaɓe, jami’an gudanarwa da masu sanya ido yadda ya kamata ba.

Ya ƙara da cewa waɗannan matsaloli sun sa jama’a da masu ruwa da tsaki suka rasa amincewa da tsarin zaɓukan fidda gwani a jihar.

Sai dai duk da kauracewar tasa, Sanata Alkali ya jaddada biyayyarsa ga jam’iyyar APC tare da bayyana aniyarsa ta ci gaba da mara wa jam’iyyar baya domin samun nasara a babban zaɓen shekarar 2027.

Haka kuma ya yi kira ga shugabannin APC na ƙasa da su soke zaɓukan da aka gudanar a yankunan da ake korafi a kansu, tare da kafa wani kwamiti na musamman domin gudanar da sahihin zaɓe cikin gaskiya da adalci.

Sanata Alkali ya kuma gode wa magoya bayansa da al’ummar jihar Gombe bisa haƙuri da natsuwar da suke nunawa duk da halin da ake ciki.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Zargin Tauye Ka’idojin Zabe: Malam Pantami Ya Janye Daga Takara
Next Post: Najeriya Da Poland Za Su Hada Kai Kan Tsaro da Bunƙasa Tattalin Arziki

Karin Labarai Masu Alaka

Menene Illar Yada Labaran Karya A Kafofin Sada Zumunta Na Zamani Labarai
An Gudanar Da Zanga-Zanga A Kasar Somaliya Labarai
Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Fadar Sarkin Musulmi: Talata Ne 1 Ga Watan Sha’aban Na 1447AH Najeriya
Kamfanonin Jiragen Sama Suna Fama Da Karin Farashin Mai Labarai
Hukumomin Bada Agaji Sun Fadakar Da Al’ummar Jihar Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jirgin Sojin Saman Najeriya Yayi Hatsari a Jihar Neja Labarai
  • Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
  • Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA. Labarai
  • “Hotuna” An Sako Daliban Makarantar St. Mary’s Su 100 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gobara Ta Tashi A Hukumar FIRS Dake Abuja Najeriya
  • Kasashe Biyar Zasu Tura Sojoji Domin Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya A Gaza Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
  • An Tsinto Gawarwakin ‘Yan gudun Hijira A Bakin Tekun Comoros Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.