Sanata Sa’idu Ahmed Alkali ya sanar da kauracewa shiga zaɓen fidda gwani na gwamnan jihar Gombe ƙarƙashin jam’iyyar APC, wanda aka shirya gudanarwa ranar Alhamis 21 ga watan Mayun 2026.
A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Umar Alkali Jibrin ya fitar, Sanatan ya ce ya ɗauki matakin ne sakamakon abin da ya bayyana a matsayin rashin gaskiya da kuma take dokokin zaɓe a zaɓukan fidda gwani na kujerun Majalisar Wakilai da na Majalisar Dattawa da aka gudanar a wasu sassan jihar.
Sanarwar ta ce zaɓukan da aka gudanar a mazabun Gombe, Kwami da Funakaye da Billiri da Balanga, da kuma Yankin Sanatan Gombe ta Tsakiya, sun kasance cike da maguɗi, rashin bayyana gaskiya da kuma rashin bin ƙa’idojin da Dokar Zaɓe ta 2026 da kundin tsarin jam’iyyar APC suka tanada.
Sanata Alkali Wanda shine Tsohon Ministan Sufurin Najeriya, ya bayyana cewa an sanar da sakamakon wasu zaɓukan ba tare da gudanar da sahihin zaɓe ba, inda ya ce an gudanar da tsarin ba tare da kayan zaɓe, jami’an gudanarwa da masu sanya ido yadda ya kamata ba.
Ya ƙara da cewa waɗannan matsaloli sun sa jama’a da masu ruwa da tsaki suka rasa amincewa da tsarin zaɓukan fidda gwani a jihar.
Sai dai duk da kauracewar tasa, Sanata Alkali ya jaddada biyayyarsa ga jam’iyyar APC tare da bayyana aniyarsa ta ci gaba da mara wa jam’iyyar baya domin samun nasara a babban zaɓen shekarar 2027.
Haka kuma ya yi kira ga shugabannin APC na ƙasa da su soke zaɓukan da aka gudanar a yankunan da ake korafi a kansu, tare da kafa wani kwamiti na musamman domin gudanar da sahihin zaɓe cikin gaskiya da adalci.
Sanata Alkali ya kuma gode wa magoya bayansa da al’ummar jihar Gombe bisa haƙuri da natsuwar da suke nunawa duk da halin da ake ciki.


