Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Kungiyar MDD Ta Bukaci Ayi Bincike Game Da Kashe ‘Yan Iran
Published: January 26, 2026 at 7:39 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar kula da hakkin Bil’adama ta MDD tayi Allah wadai da kasar Iran ko Farisa a ranar jumma’a, kan keta hakkin Bil’adama, kuma ta bukaci da a gudanar da bincike kan murkushe masu zanga-zanga, mataki da ya halaka dubban mutane.

Shugaban hukumar, Volker Turk, wanda ya gayawa wakilan hukumar abubuwa da suka faru a Iran, a taron ta da aka yi a birnin Geneva, ya bayyana damuwarsa kan makomar wadanda hukumomin Iran suka kama lokacin zanga zangar.

Hukumar ta amince da wani kuduri da zai fadada kudurin da ta amince dashi tun a shekara 2022 na gudanar da bincike ciki har da na yanzu, da zummmar daukar mataki nan gaba.

Iran tayi Allah wadai da wannan mataki, tana mai cewa an tsoma siyasa cikin lamarin, tana ta nanata matakan gudanar da bicike, tace wannan mataki shishshige ne cikin harkokin cikin gida. Ta kuma aza laifin tarzomar “kan ‘yan ta’adda, da masu neman tada zaune tsaye, wadanda take zargi, kan ‘yan adawar gwamnattin kasar daga ketare da kuma kasashen Amurka da Isra’ila.

Kasashe 25 ne suka amince da wannan kuduri cikin su har da Faransa, da Mexico, da koriya ta kudu, yayinda kasashe bakwai ciki harda China, da India suka ki goyon bayan kudurin, wasu kasashe 14 kuma suka kauracewa jefa kuri’a.

Kasashen China, da Pakistan, da Ethiopia, duk sun bayyana rashin gamsuwa da tasirin zaman hukumar, har jakadan China a hukumar ya kira batun, “alamarin cikin gida ne na Iran.

Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Jirgin Ruwan ‘Yan Gudun Hijira Ya Nitse Kogi A Tunisiya
Next Post: Harin Isra’ila A Gaza Da Jirgi Maras Matuki Ya Kashe Mutane

Karin Labarai Masu Alaka

PDP Ta Nemi Bincike Kan Rushewar Ginin Majalisar Dokokin Gombe, Tayi Zargi Game Da Sakaci Labarai
Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
Kotu A Kasar Tunisiya Ta Daure Wani Babban Dan Kasuwa Da Wasu ‘Yan Majalisa Afrika
NSCIA Ta Gargadi Gwamnati Kan Zargin Tauye Haƙƙin Musulmi Afrika
Kasar Faransa Zata Bunkasa Nukiliyarta Afrika
Gwamnatin Tarayyar Najeriya Zata Raba Taki Ga Manoma Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sama Da Zawiyya 100 Ne Suka Samu Tallafin Kayan Abinci Daga Al’mustapha Haji Sufi Labarai
  • Farashin Mai Yana Cigaba Da Karuwa Afrika
  • Kwankwaso Yayi Kakkausar Lafazi Bayan Ficewar Abba Kabir Yusuf Daga NNPP Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gidauniya: An Fara Tiyatar ‘Hernia’ Da ‘Hydrocele’ Kyauta A Jihar Katsina Labarai
  • Musa: “Da Yaddar Allah Zamu Ga Bayan Ta’addanci A Najeriya” Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Wani Dan Bindiga Ya Harbi Dakarun Tsaron Cikin Gida Su Biyu A Washington DC Labarai
  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala Afrika
  • An Bukaci Matasa Su Taka Gagarumar Rawa Wajen Gina Zaman Lafiya A Arewa Maso Gabas Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.