Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Kungiyar MDD Ta Bukaci Ayi Bincike Game Da Kashe ‘Yan Iran
Published: January 26, 2026 at 7:39 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumar kula da hakkin Bil’adama ta MDD tayi Allah wadai da kasar Iran ko Farisa a ranar jumma’a, kan keta hakkin Bil’adama, kuma ta bukaci da a gudanar da bincike kan murkushe masu zanga-zanga, mataki da ya halaka dubban mutane.

Shugaban hukumar, Volker Turk, wanda ya gayawa wakilan hukumar abubuwa da suka faru a Iran, a taron ta da aka yi a birnin Geneva, ya bayyana damuwarsa kan makomar wadanda hukumomin Iran suka kama lokacin zanga zangar.

Hukumar ta amince da wani kuduri da zai fadada kudurin da ta amince dashi tun a shekara 2022 na gudanar da bincike ciki har da na yanzu, da zummmar daukar mataki nan gaba.

Iran tayi Allah wadai da wannan mataki, tana mai cewa an tsoma siyasa cikin lamarin, tana ta nanata matakan gudanar da bicike, tace wannan mataki shishshige ne cikin harkokin cikin gida. Ta kuma aza laifin tarzomar “kan ‘yan ta’adda, da masu neman tada zaune tsaye, wadanda take zargi, kan ‘yan adawar gwamnattin kasar daga ketare da kuma kasashen Amurka da Isra’ila.

Kasashe 25 ne suka amince da wannan kuduri cikin su har da Faransa, da Mexico, da koriya ta kudu, yayinda kasashe bakwai ciki harda China, da India suka ki goyon bayan kudurin, wasu kasashe 14 kuma suka kauracewa jefa kuri’a.

Kasashen China, da Pakistan, da Ethiopia, duk sun bayyana rashin gamsuwa da tasirin zaman hukumar, har jakadan China a hukumar ya kira batun, “alamarin cikin gida ne na Iran.

Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Jirgin Ruwan ‘Yan Gudun Hijira Ya Nitse Kogi A Tunisiya
Next Post: Harin Isra’ila A Gaza Da Jirgi Maras Matuki Ya Kashe Mutane

Karin Labarai Masu Alaka

Masana Lafiya – Preeclampsia Cuta Ce Mai Hadari Amma Ana Iya Magance Ta Afrika
Shugaban Miyetti Allah Zai Fuskanci Shari’a Kan Zargin Badakalar Kuɗi da Ta’addanci Afrika
Jihar Gombe Ta Karbi Bakuncin Taron Tsaro Tsakanin DIG Da Masu Ruwa Da Tsaki Afrika
Amurka Zata Bada Gudunwa Ga Masu Zanga-Zanga A Iran Sauran Duniya
Isra’ila Ta Zantar Da Hukuncin Kisa Ga Masu Kai Hare Hare Labarai
‘Yan Bindiga A Mali Sun Kashe Direbobin Manyan Motoci Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe Afrika
  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Taki Da Mai Ga Manoma Labarai
  • Anyi Girgizar Kasa Mai Karfi A Kasar Mexico Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hukumomin Tsaron Kenya Sunce ‘Yan Kasar Suna Fafata Yaki Da Dakarun Rasha A Ukraine Afrika
  • Netanyahu Yana Neman Shawarwari Daga Hukumomin Lebanon Labarai
  • Ambaliyar Ruwa Ya Tilastawa Dubban Jama’a Rasa Muhallensu A Morocco Afrika
  • Jirgi Marar Matuki Yayi Ajalin A Kallah Mambobin M23 9 Tare Da Kashe Kakakin Rundunar Afrika
  • Ana Cigaba Da Yaki Tsakanin Amurka Da Isra’ila Da Kasar Iran Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.