Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
Published: April 16, 2026 at 8:59 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jami’an Rundunar Karewa Al’umma a jihar Zamfara, da aka fi sani da “Askarawa”, sun kama wasu na’urorin fashewa, makudan kuɗaɗe, da sauran kayan tallafi da ake zargin za’a kaiwa ’yan bindiga a ƙauyen Bindin da ke Ƙaramar Hukumar Maru.

Kwamandan rundunar CPG na jihar, AIG Shehu Muhammad Dalijan (mai ritaya), ya bayyana hakan yayin da yake gabatar da waɗanda ake zargi tare da kayayyakin da aka ƙwato ga manema labarai a hedikwatar rundunar da ke Gusau.

Ya ce wannan nasara ta biyo bayan sahihan bayanan sirri da suka nuna cewa wata mota mai ɗauke da kaya ta tashi daga Danhasiya Plaza da ke Gusau zuwa ƙauyen Bindin, yankin da ake zargin yana ƙarƙashin ikon ’yan bindiga.

A cewarsa, jami’an sun tare motar mai lamba KMC 120-XR, inda suka kama direban tare da wasu mutane shida kuma ayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da kuɗi Naira miliyan 13,352,500, abubuwan fashewa 98 na na’urorin gargajiya (IEDs) da ake zargin dynamite ne, na’urorin tayar da fashewa guda 25, babura sababbi guda uku, wayoyin Android, sigari, ’ya’yan itacen tuffa, jarkoki huɗu na dizal, jarkoki uku na man ja, da kuma kayan haƙa kamar felaye da cokula.

Dalijan ya ce za a miƙa waɗanda aka kama tare da kayayyakin ga ’yan sanda domin ci gaba da bincike da kuma gurfanar da su a gaban kotu.

A cikin bayaninsa, direban motar, Abubakar Abdullahi Dangulbi, ya ce wani mai suna Aliyu Labaran ne ya ɗauke shi aiki domin kai kuɗin ga wani Alhaji Abubakar Bindin daga hannun wani Nasiru Dan Zuru (wanda ke tsere), yayin da aka ce na’urorin fashewar na wani Jamilu Lingyado ne a ƙauyen Bindin, Sai kuma yace bai san abin da ke cikin kayan ba, yana mai jaddada cewa shi aikin kai saƙo kawai aka ba shi.

“Ban san abin da ke cikin kayan ba. An ba ni aikin kai su ne kawai ga masu su a Bindin,” in ji shi.

Dalijan ya yi gargaɗi cewa matsalar tsaro da ke addabar jihar Zamfara na samun ƙarfi ne daga masu haɗin gwiwa da ke samar wa ’yan bindiga kayan aiki, bayanan sirri da sauran tallafi, ya kuma jaddada cewa irin waɗannan na’urorin fashewa na iya jawo asarar rayuka masu yawa ga fararen hula da jami’an tsaro.

Ya ƙara da cewa rundunar CPG za ta ci gaba da ƙara ƙaimi wajen yaƙi da masu aikata laifuka, tare da tabbatar da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin jihar.

Haka kuma, ya yaba wa gwamnatin jihar Zamfara kan tallafin kayan aiki da take bayarwa, yana mai cewa za a yi amfani da su yadda ya kamata wajen yaƙi da ’yan bindiga.

Wannan nasara ta ƙara nuna damuwa a tsakanin masana harkar tsaro cewa matsalar ’yan bindiga a Zamfara na ƙara samun goyon baya ta hanyar tsare-tsaren samar da kayayyaki masu ƙarfi, lamarin da ke buƙatar ƙarin tsauraran matakan sa ido da kuma katse hanyoyin samar da irin waɗannan kayayyaki.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
Next Post: Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
Ambaliyar Ruwa Yayi Ajalin Mutane A Nairobi Afrika
Gwamnatin Tinubu Zata Gyara Hanyar Akwanga Zuwa Jos Labarai
Farashin Danyen Mai Ya Fadi A Kasuwar Duniya Afrika
An Kaddamar Da Rigakafin Cutar HIV AIDS A Kasar Zimbabwe Kimiya
Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero
  • Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa
  • Gwamnatin Najeriya Zata Rabawa Al’umma Tallafin Noma
  • Shugaba Trump Ya Yabawa Iran Bisa Bude Mashigar Hormuz

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Da Iran Sun Tattauna A Kasar Pakistan Afrika
  • Gwamnatin Gombe Ta Dauki Sabbin Matakan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Rundunar Sojin Najeriya Ta Dakile Harin ‘Yan Ta’adda A Jihar Borno Labarai
  • Rundunar Tsaro Suna Cigaba Da Nasara Akan ‘Yan Ta’adda Tsaro
  • Jami’ar Tarayya A Gombe Ta Karyata Harin ‘Yan Bindiga Najeriya
  • Ukraine Tana Cigaba Da Tattaunawa Da Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Kasar Amurka
  • Samar Da Tsaro A Jihar Kano Ba Sai An Sa Siyasa Ba! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Tana Cigaba Da Korar Baki Daga Amurka Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.