Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Jami’an Askarawa A Zamfara Sun Kama Na’urorin Fashewa Da Makudan Kuɗaɗe
Published: April 16, 2026 at 8:59 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jami’an Rundunar Karewa Al’umma a jihar Zamfara, da aka fi sani da “Askarawa”, sun kama wasu na’urorin fashewa, makudan kuɗaɗe, da sauran kayan tallafi da ake zargin za’a kaiwa ’yan bindiga a ƙauyen Bindin da ke Ƙaramar Hukumar Maru.

Kwamandan rundunar CPG na jihar, AIG Shehu Muhammad Dalijan (mai ritaya), ya bayyana hakan yayin da yake gabatar da waɗanda ake zargi tare da kayayyakin da aka ƙwato ga manema labarai a hedikwatar rundunar da ke Gusau.

Ya ce wannan nasara ta biyo bayan sahihan bayanan sirri da suka nuna cewa wata mota mai ɗauke da kaya ta tashi daga Danhasiya Plaza da ke Gusau zuwa ƙauyen Bindin, yankin da ake zargin yana ƙarƙashin ikon ’yan bindiga.

A cewarsa, jami’an sun tare motar mai lamba KMC 120-XR, inda suka kama direban tare da wasu mutane shida kuma ayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da kuɗi Naira miliyan 13,352,500, abubuwan fashewa 98 na na’urorin gargajiya (IEDs) da ake zargin dynamite ne, na’urorin tayar da fashewa guda 25, babura sababbi guda uku, wayoyin Android, sigari, ’ya’yan itacen tuffa, jarkoki huɗu na dizal, jarkoki uku na man ja, da kuma kayan haƙa kamar felaye da cokula.

Dalijan ya ce za a miƙa waɗanda aka kama tare da kayayyakin ga ’yan sanda domin ci gaba da bincike da kuma gurfanar da su a gaban kotu.

A cikin bayaninsa, direban motar, Abubakar Abdullahi Dangulbi, ya ce wani mai suna Aliyu Labaran ne ya ɗauke shi aiki domin kai kuɗin ga wani Alhaji Abubakar Bindin daga hannun wani Nasiru Dan Zuru (wanda ke tsere), yayin da aka ce na’urorin fashewar na wani Jamilu Lingyado ne a ƙauyen Bindin, Sai kuma yace bai san abin da ke cikin kayan ba, yana mai jaddada cewa shi aikin kai saƙo kawai aka ba shi.

“Ban san abin da ke cikin kayan ba. An ba ni aikin kai su ne kawai ga masu su a Bindin,” in ji shi.

Dalijan ya yi gargaɗi cewa matsalar tsaro da ke addabar jihar Zamfara na samun ƙarfi ne daga masu haɗin gwiwa da ke samar wa ’yan bindiga kayan aiki, bayanan sirri da sauran tallafi, ya kuma jaddada cewa irin waɗannan na’urorin fashewa na iya jawo asarar rayuka masu yawa ga fararen hula da jami’an tsaro.

Ya ƙara da cewa rundunar CPG za ta ci gaba da ƙara ƙaimi wajen yaƙi da masu aikata laifuka, tare da tabbatar da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin jihar.

Haka kuma, ya yaba wa gwamnatin jihar Zamfara kan tallafin kayan aiki da take bayarwa, yana mai cewa za a yi amfani da su yadda ya kamata wajen yaƙi da ’yan bindiga.

Wannan nasara ta ƙara nuna damuwa a tsakanin masana harkar tsaro cewa matsalar ’yan bindiga a Zamfara na ƙara samun goyon baya ta hanyar tsare-tsaren samar da kayayyaki masu ƙarfi, lamarin da ke buƙatar ƙarin tsauraran matakan sa ido da kuma katse hanyoyin samar da irin waɗannan kayayyaki.

Afrika, Labarai, Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
Next Post: Shugaba Tinubu Yace Bazai Bawa ‘Yan Najeriya Kunya Ba

Karin Labarai Masu Alaka

Prime Ministan Pakistan Yace Zai Karbi Bakoncin Tattaunawar Amurka Da Iran Afrika
Dottin Shara Ya Damu Jama’ar Havana Kasar Cuba Labarai
Jirgin Ruwa Ya Kife A Yammacin Kasar Gambiya Labarai
Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci Afrika
Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
Za’a Ninka Shekarun Kurkuku Ga Masu Aikata Luwadi A Senegal Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Masu Luwadi Na Fuskantar Tara Da Daurin Shekaru 20 A Nijar Afrika
  • Shugaban Kasar Ivory Coast Yayi Sauye-Sauye A Majalisar Ministocin Kasar Siyasa
  • GoHealth Ta Buɗe Sabon Babin Kula Da Lafiya Ta Hanyar Fasaha Afrika
  • Jami’an Diflomasiyyar Iran Dana Amurka Sun Tattauna A Kasar Oman Afrika
  • NEDC Ta Fara Shirin Kera Sanitary Pads A Gombe Domin Samar Da Sana’o’i Afrika
  • Kungiyar ‘Yan Ta’adda Masu Alaka Da ISIS Sun Kashe Mutane A Congo Tsaro
  • Gasar Cin Kofin Nahiyar Afrika A Wannan Makon Wasanni
  • Kasashen Amurka,Israela Da Iran Sun Amince Da Dakatar Da Yaki Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.