Gwamnatin Tarayya ta sake jaddada aniyarta na yaƙi da talauci tare da samar da hanyoyin inganta rayuwar ’yan ƙasa, musamman ma mazauna karkara waɗanda ayyukan ci gaba ba su cika isa gare su ba.
Babban Manajan Shirin GEEP 3.0 na “FarmerMoni” karkashin tsarin ‘Renewed Hope’, Hamza Ibrahim-Baba, shi ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi yayin taron wayar da kan kafofin yaɗa labarai na shiyyar Arewa maso Yamma da aka gudanar a birnin Kano.
Ibrahim-Baba ya bayyana cewa wannan shiri na RH-GEEP 3.0, wanda ya shafi manoman rani da na damina, wani ɓangare ne na manufofin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na farfaɗo da tattalin arziƙin ƙananan sana’o’i a faɗin ƙasar nan.
Ya ce: “An tsara GEEP 3.0 ne domin ya isa zuwa ga al’ummar da aka bari a baya, da kuma inganta tattalin arziƙi tun daga tushe. Burinmu shi ne mu tallafa wa ’yan Nijeriya da ke can ƙasan matattarar tattalin arziƙi, mu inganta rayuwarsu, kuma mu samar musu da damar samun kudin shiga mai dorewa.”
A nata jawabin, Darakta Janar ta Hukumar Kare Muradin Jama’a ta Jihar Kano, Fatima Abubakar-Abdullahi, ta bayyana cewa shirin ya sa gaba ne wajen tallafa wa rukunin mutanen da suka fi rauni, musamman manoma da ƙananan ’yan kasuwa na karkara.
Ta ƙara da cewa shirin zai samar da damar samun rance ba tare da ruwa ba, tare da bayar da horon gina ƙwarewa ga masu cin gajiyar shirin.
Haka zalika, ta jaddada mahimmancin wayar da kai, inda ta nuna cewa da yawa daga cikin waɗanda suka cancanci shirin ba su riga sun fahimci hanyoyin da za su bi domin cin gajiyar sa ba.
“Irin wannan wayar da kan na da mahimmanci matuƙa. Idan mutane suka fahimci yadda shirin yake tafiya, shiga cikinsa zai ƙaru, sannan tasirinsa zai kasance mai ma’ana ga rayuwarsu,” in ji ta.


