Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci
Published: April 27, 2026 at 10:48 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayya ta sake jaddada aniyarta na yaƙi da talauci tare da samar da hanyoyin inganta rayuwar ’yan ƙasa, musamman ma mazauna karkara waɗanda ayyukan ci gaba ba su cika isa gare su ba.

Babban Manajan Shirin GEEP 3.0 na “FarmerMoni” karkashin tsarin ‘Renewed Hope’, Hamza Ibrahim-Baba, shi ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi yayin taron wayar da kan kafofin yaɗa labarai na shiyyar Arewa maso Yamma da aka gudanar a birnin Kano.

Ibrahim-Baba ya bayyana cewa wannan shiri na RH-GEEP 3.0, wanda ya shafi manoman rani da na damina, wani ɓangare ne na manufofin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na farfaɗo da tattalin arziƙin ƙananan sana’o’i a faɗin ƙasar nan.

Ya ce: “An tsara GEEP 3.0 ne domin ya isa zuwa ga al’ummar da aka bari a baya, da kuma inganta tattalin arziƙi tun daga tushe. Burinmu shi ne mu tallafa wa ’yan Nijeriya da ke can ƙasan matattarar tattalin arziƙi, mu inganta rayuwarsu, kuma mu samar musu da damar samun kudin shiga mai dorewa.”

A nata jawabin, Darakta Janar ta Hukumar Kare Muradin Jama’a ta Jihar Kano, Fatima Abubakar-Abdullahi, ta bayyana cewa shirin ya sa gaba ne wajen tallafa wa rukunin mutanen da suka fi rauni, musamman manoma da ƙananan ’yan kasuwa na karkara.

Ta ƙara da cewa shirin zai samar da damar samun rance ba tare da ruwa ba, tare da bayar da horon gina ƙwarewa ga masu cin gajiyar shirin.

Haka zalika, ta jaddada mahimmancin wayar da kai, inda ta nuna cewa da yawa daga cikin waɗanda suka cancanci shirin ba su riga sun fahimci hanyoyin da za su bi domin cin gajiyar sa ba.

“Irin wannan wayar da kan na da mahimmanci matuƙa. Idan mutane suka fahimci yadda shirin yake tafiya, shiga cikinsa zai ƙaru, sannan tasirinsa zai kasance mai ma’ana ga rayuwarsu,” in ji ta.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci
Next Post: Majalisa Ta Tabbatar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan Kano

Karin Labarai Masu Alaka

Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
Kasashen Amurka,Israela Da Iran Sun Amince Da Dakatar Da Yaki Afrika
Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutu Najeriya
An Kai Hari Babbar Tashar Iskar Gas A Iran Afrika
An Kashe Mutane 169 A Wani Harin Sudan Ta Kudu Afrika
Yaki Ta Sararin Samaniya Ya Cigaba Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Farfesa Inuwa Ja’afaru Yakarbi Ragamar Shugabancin Jami’ar Kashere Labarai
  • Rikici Ya Barke A Kano Bayan Kashe Wani Matashi Da Ake Zargi Da Kashe Ladani Najeriya
  • Dakarun Sakai A Kasar Sudan Sun Kashe Mutane 28 A Wani Farmaki Afrika
  • Za’a Jima Ana Fama Da Tsadar Farashin Mai Afrika
  • Kungiyar ISIS Ta Dauki Alhakin Harin Kasar Nijar Afrika
  • ‘Yansandan Uganda Sun Tsare ‘Yar Fafutukar Kare Hakkin Bil’adama Sarah Bireete Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Motar Kungiyar Kwallon Kafar Bayelsa United Ta Yi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Kusa Kawo Karshen Matsalolin Tsaro A Jihar Filato Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.