Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa Afrika
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa Afrika
  • Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane Afrika
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Afrika
  • Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo Ya Rasu A Abuja Bayan Doguwar Jinya Afrika

Gwamnatin Najeriya Ta Jadda Da Aniyar Rage Radadin Talauci
Published: April 27, 2026 at 10:48 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Tarayya ta sake jaddada aniyarta na yaƙi da talauci tare da samar da hanyoyin inganta rayuwar ’yan ƙasa, musamman ma mazauna karkara waɗanda ayyukan ci gaba ba su cika isa gare su ba.

Babban Manajan Shirin GEEP 3.0 na “FarmerMoni” karkashin tsarin ‘Renewed Hope’, Hamza Ibrahim-Baba, shi ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi yayin taron wayar da kan kafofin yaɗa labarai na shiyyar Arewa maso Yamma da aka gudanar a birnin Kano.

Ibrahim-Baba ya bayyana cewa wannan shiri na RH-GEEP 3.0, wanda ya shafi manoman rani da na damina, wani ɓangare ne na manufofin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na farfaɗo da tattalin arziƙin ƙananan sana’o’i a faɗin ƙasar nan.

Ya ce: “An tsara GEEP 3.0 ne domin ya isa zuwa ga al’ummar da aka bari a baya, da kuma inganta tattalin arziƙi tun daga tushe. Burinmu shi ne mu tallafa wa ’yan Nijeriya da ke can ƙasan matattarar tattalin arziƙi, mu inganta rayuwarsu, kuma mu samar musu da damar samun kudin shiga mai dorewa.”

A nata jawabin, Darakta Janar ta Hukumar Kare Muradin Jama’a ta Jihar Kano, Fatima Abubakar-Abdullahi, ta bayyana cewa shirin ya sa gaba ne wajen tallafa wa rukunin mutanen da suka fi rauni, musamman manoma da ƙananan ’yan kasuwa na karkara.

Ta ƙara da cewa shirin zai samar da damar samun rance ba tare da ruwa ba, tare da bayar da horon gina ƙwarewa ga masu cin gajiyar shirin.

Haka zalika, ta jaddada mahimmancin wayar da kai, inda ta nuna cewa da yawa daga cikin waɗanda suka cancanci shirin ba su riga sun fahimci hanyoyin da za su bi domin cin gajiyar sa ba.

“Irin wannan wayar da kan na da mahimmanci matuƙa. Idan mutane suka fahimci yadda shirin yake tafiya, shiga cikinsa zai ƙaru, sannan tasirinsa zai kasance mai ma’ana ga rayuwarsu,” in ji ta.

Afrika, Labarai, Najeriya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci
Next Post: Majalisa Ta Tabbatar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan Kano

Karin Labarai Masu Alaka

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Sojoji 15 Da Wasu Fararen Hula A Benin Afrika
Hamas Ta Kwance Damara Afrika
Shugabar Hamayya A Venezuela Ta Gana Da Paparoma Leo Amurka
Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Netanyahu Ya Umarci Rundunar Sojoji Takara Fadada Ayyukanta A Lebanon Afrika
Dakaru Sun Hallaka ’Yan Ta’adda Masu Yawa – DHQ Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Hukumar Raya Birane Ta Rushe Gine-Ginen Da Suka Keta Dokokin Tsara Birane A Gombe
  • Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa
  • Ahmed Gara Ya Kaddamar da Kofin Sarkin Gombe, Ya Jaddada Bunƙasa Matasa
  • Janar Rabe Abubakar Ya Mutu A Tsare A Hannun Masu Garkuwa Da Mutane
  • Anyi Jana’izar Dan Majalisar Wakilai Yaya Bauchi Tongo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • “Yan Wasan Super Eagles Sun Karbi Alkawarin Da Gwamnati Tayi Musu AFCON 2023 Labarai
  • Domin Karfafa Tsaro Babban Hafsan Sojin Najeriya Ya Ziyarci Jos Afrika
  • Ana Gudanar Da Zanga-Zangar Adawa Da Gwamnati A Kasar Tunisiya Siyasa
  • Yarjejeniyar Britaniya Da Mauritius Kan Tsibiran Chagos Cin Zarafi Ne Labarai
  • Amurka Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Fara Wata Tattaunawa Afrika
  • Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai
  • Kasar Zimbabwe Ta Samar Da Dokar Tsawaita Mulkin Mnangagwa Zuwa 2030 Labarai
  • Rikici Ya Lafa A Kasar Iran Bayan Daukar Matakai Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.